NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 59 of 97

an suna tare da mahaifiyarsa. Yanzunma kallo su ke yi sai dai ita da shi suna hira jefi jefi, yaran ne hankalinsu ya tattara ga tv, nayi sallama su ka ɗago su ka kalleni, a daƙile Iyam ta amsa shi kuwa sai tsareni da ido yay, sannu da hutawa nayi mata domin mun rigada mun gaisa tun ɗazu, na tambayeta abinda take so a dafa da rana tace faten tsaki amma yaji gyaɗa da ganye na ce to, miƙewa nayi na wucewata kitchen ban bi ta kansa ba da bakinsa da naga yana son magantuwa da alama. tun zuwanta na daina dafa son ran kowa sai na tambayeta me take so a girka, har ga Allah jinta na ke yi kamar uwata, kullum ƙoƙarina in kyautata mata amma sam ba na tsira, komai na yi bana burgeta balle yay mata daɗi, burinta ta kushe ni kawai, ku san kullum sai ta faɗa min bata sona bata son zamana da ɗanta, maganar tun tana damuna ma har na daina jinta, takurawar da baiwar Allah nan ke min yayi yawa, ta hana ni shan iska kwata kwata, ta hana na huta na sake, magana tsakaninta da ni daga gori sai cin mutunci da zarafi, kuma duk wannan abubuwan da take min daidai da rana guda ban ji ina so na mata rashin kunya ba ko na ƙi bin umarninta, uwa ce ita ko bata haife ni ba ta haifi mijina. ina tsaka da aiki sai ga shi ya shigo kitchen ɗin, tun kallo ɗaya da na masa na watsar, ya shiga dube duben da zai yi, ni na san babu abinda ya shigo da shi sai don dai yay min magana kawai. kusan minti ɗaya yana faman bulayin iska ganin na basar da shi sai ce yayi,"babu abunda ake buƙata?". kamar bazan amsa shi ba sai can na ce,"babu". "komai akwai?". na ce,"ummm". shiru yayi na ƴan sakanni sannan ya sake cewa,"ki saka daddawa da yawa a ciki bata son fate babu daddawa". na ce,"na sani ai". ina jin kallonsa a jikina har ya fice a kitchen ɗin. bayan na kammala girkin Iyam na fara zubawa na kai mata ɗakinta, na zo ina zubawa yaran nasu sai ƙwala kiranta naji, naje da hanzari gareta cike da ladabi da girmamawa. flask ɗin abincin ta turo gabana tana cewa,"wannan abincin na ki ai kin cika tafarnuwa tayi wani bauuu, ni kuwa kin san idan tayi yawa bana iya ci. ɗauki kije kawai idan anyi na dare na ci". shiru nayi na kasa motsi, wai tafarnuwa! ni da rabon da nayi girki ma da tafarnuwa har na manta, tun farkon zuwan su Atika na daina amfani da ita saboda Rumana bata ci, kawai dai saboda ta janyo min faɗa wurin ɗanta, kuma yanzu na san ba komai yasa ta yin hakan ba sai ganin zan fita ne, tunda a gabanta na tambaye shi ya ce naje amma kar nayi yamma, to fitar ce bata so idan na ɓata lokaci sai yace in fasa ranta yay fari. na sauke numfashi na ce,"to me zan ƙara dafa miki?". "a'a ke da kike sauri za ki fita ai bana ƙara sa ki wahala ba". nayi murmushi na ce,"fitar ba ta fiki muhimmanci ba, in dai fita ce kam sai na haƙura da ita akanki. don Allah ki faɗa min me zan dafa miki babu wahala ga aikin uwa". "soya min wainar fulawa, amma kar kisa taruhu me yawa kuma albasa taji sosai". na ce,"tou". kana na miƙe na tashi na fita. har na sa a raina na haƙura da fitar sai ga shi kuma na gama suyar da wuri. na kawo mata fuska babu yabo babu fallasa tace an gode Allah yay albarka, naji daɗin adu'ar da tayi min karon farko tun zuwanta gidan. na fita na koma kitchen ɗin na kwaso nasa kayan abincin sannan na wuce zuwa ɗakinsa. yana shirin fitowa muka yi kiciɓis tray ɗin hannuna ya kusa faɗuwa yay saurin tareni. bai bani hanya na wuce ba ni kuma ban ce masa kanzil ba tunda dai ai yana da ido, hannuna ne dai ya ƙage saboda nauyin kwanukan cikin tray ɗin, yay tsaye akaina kaman wani sanda, ganin tsayuwar tasa ba me ƙarewa ba ce na raɓa ta ɗan tsukukun gefensa na wuce, na shimfiɗa carpet ɗin da yake cin abinci akai tukunna na ɗora masa kayan abincin. Shi kuwa baki buɗe ya ke kallonta, ta raɓa shi ta wuce har tana noƙe jikinta saboda wulaƙanci, bai san nufinta ba da wannan zaman da ta tsira tsakaninsu, tana ta wani shareshi tsabar raini, ga dai shi tana sakin jiki da mahaifiyarsa wani sa'in ma da yaran, amma shi sai wani nuna halin ko in kula take masa, da sun haɗa ido sai ta haɗe rai tana faman ciccin magani, ta mayar da shi kamar wani ɗan iska sai yake magana tana amsa masa a daƙile, shiyasa yake ganin kaman ba ita ba an sauyata, don mamakinya ke sosai akan canjawarta, kuma ya ɗaga mata ƙafa ne kawai don yaga iya gudun ruwanta, sai dai ya lura idan bai yiwa tufkar hanci ba haka za'a ci gaba da tafiya, zata mayar da shi shashashan miji ta bakin Iyam, kusan satika nawa ko ta hakkinsa ma ba ta bi, ko so take har sai ya nuna mata cewa ya gaji yana da buƙatar kasancewa da ita ne, yanayinta sam ma ba ya nuna tana da damuwa yanzu da shi, tayi wani haske ƙirjinta ya cika, ko faɗa yay mata yanzu sai ta ɗau fushi da shi saɓanin da da hankalinta zai ta shi ta rasa sukuni, lallai yay sake ta yawa. ina sauke ajiyar zuciya ta gajiya na dubi inda yake na ce,"ga abincinka in zuba ya
🏠