haÆurina da sanyina a gefe na Éan wani lokaci in fara rama abin da ake min hakan zai saka duk su saduda, amma wannan haÆurin da na ke shi ke basu lasisin ci min fuska har shi mijin. saboda haka na aro rigar rashin mutunci da masifa da bala'i in saka in zama kamar wuta saboda zafin rai, in ci kutumar uban duk Éan iskan da yay min ko da kallon banza ne balle ya nemi ya gaya min magana, ta ce harta uwarsa kar in raga mata, ÆarÆari in koyi kissa in yi kaman zan mata sujjada a gabansa amma a bayan idonsa in nuna mata karrr na ke bani da mutunci ko Æwas, idan na fara hakan za su rabu da ni su kama abun da yake gabansu nima in huta.
na ji shawarartata na Éan hau kan wata, tun da lallaÉawa na ke kar na zaÆe da yawa ya kuma kai Æarata gidanmu in shiga uku. yanzun dai yadda nake haÉe rai idan na gansa har shakkar yi min magana yake, na fita harkarsa gaba Éaya na cire tsoro sai ya fara mamakina hakan kuma ya dame shi, ya fara neman shishshige min yana neman shiri, ni kuwa sam naÆi basa fuska na nuna masa nima mutum ce me zuciya a Æirji. ko fita zai yi bana damuwa da in bisa in masa a dawo lafiya, sai ga shi in yaga dama wani lokacin idan zai fita ya zo yace min zai fita, ba kuwa na Éaga ko gashin gira na kalli inda ya ke, hatta Éakinsa yanzu tsakanina da shi in kai masa abinci da na gama gyara kuma sai washegari, karatu ma sai na so nake zama yay min, ranar nan babu yanda bai da ni ba akan in zo Éakinsa cikin dare nayi mursisi naÆi zuwa, domin na Æudurci ni da zuwa Éakinsa sai ranar da ya san darajata.
To haka dai na ke ta zaman babu daÉi, duk wani nawa da ya kamata ya zo gidan in gansa inji daÉi Abbaa ya hana domin da kansa yasa aka kira masa me gadi da shi Nazifin ya faÉawa me gadin duk baÆon da aka yi ya tambaye shi wurin wa ya zo, in dai wurina aka zo to kar ya bari a shiga. to Yashaik Éin ma da yake zuwa ya daina, in ya zo dai faÉa ne ke kawo shi to amma a haka na ke farin ciki.
ta Éangarensa yanzu ba na da wata matsala tunda babu abunda ke haÉamu, daga wajen Iyam ne dai da kuma Æ´an uwan nasa abun babu sauÆi matsalar ta tsananta har tafi da, sun matsa min sosai cin mutuncina su ke yanda suka so. duk abunda su ke min haka nake shanyewa in hana kaina damuwa tun da dai haihuwar ba ni zan bawa kaina ba, haka kuma shi da su ke yi akansa Éin ba ya yi min, tunda ba shi su Atika ya rage nuna damuwa akan rashin haihuwar.
Maman Yasmin kuwa ranar ta saci hanya tazo ta dinÆa faÉan maita da rashin zuciya irin nawa ne yasa na ke zaune a gidan, in bar musu gidan mana rabuwa da Nazifi ai ba shi zai hana ni Æara yin aure ba. na ce mata sam ba rashin zuciya ba ne ina gudun bakin mutane ne da kuma Éacin ran iyaye, domin duk ranar da Abbaa ya tashi zai ce min babbar biyayyar da zan masa ita ce na zauna gidan mijina, Ummani kuwa da ta tashi yi min nasiha zata fara ne da haÆuri sannan ta tafi ga batun babbar suturar Ƴa mace shine aure, kuma gidan miji shine mafi daraja wajen Æ´a mace.
Yau ya kama lahadi, na tashi da sha'awar yin jan lalle, dama zan je kitso in sha Allah daga can zan wuce ayi min ko iya hannaye ne, da yake muna da taron suna ranar laraba jiya Ummani ta kirani take faÉa min Asiya ta haihu Æ´ar Æanwar su Abbaa wacce su ke uba Éaya, haihuwar sosai ta sakani farin ciki kuma a sannan nima na cire tsammani akan ba zan taÉa haihuwa ba, domin kuwa Asiya ta riga ni aure ita shekara goma kenan sai yanzu Allah ya kawo haihuwar, babu irin tsangwamar da bata sha ba don zan iya cewa har gwara ni, tunda ita sau biyu mijin na sakinta, ga kishiya da ta sanyota gaba, da yake Allah ne mai bayarwa komai kuma Lokaci ne sai ga shi yanzu Allah ya bata, ni ma Allah yasa ina da rabo, ya bani ko don masu goranta min da ganin ni na gaza.
bayan na shirya na fito domin naje na yi ayyukan da zan yi, a falo na tarar da su gaba Éaya a zaune, dama tun zuwan Iyam gidan duk ranar Lahadi yini su ke a falo gaba Éayansu, in ba yaran ne za su wuce islamiya ba, shi kuwa tun can asali lahadi ranar hutawarsa ce da lokacin iyalinsa balle yanzu da mahaifiyarsa ke gidan, in ba masallaci ba ko Æofar gida ba ya leÆawa. ni dai in ka ganni a falon to zirga zirgar aiki ce don ba na zama balle raina ya Éaci, idan tana zaune na zo na zauna don tayata hira in ba ya nan sai ta kama faÉin kana zama tare da surukarka waje Éaya saboda rashin Éa'a, idan kuma shine zaune a falon babu ita na zo na zauna sai ta kama bambamin ai bani da kunya ba ni da tarbiya dole sai na nuna mata Æ´ar zamani ce ni, ina faman liÆewa miji alhalin na san tana zaune cikin gidan saboda dai ba na son zamanta so na ke ta bar gidan. ranar har ce tayi da shi ita akan lamarina na Æ´an iskan mata sai ta iya tattarawa ta tafi, banda tana ganinsa kusa da ita kullum hankalinta na kwanciya ai tuni ta kama gabanta, yay ta bata haÆuri ni kuma ya sameni yace ko magana na ke son yi da shi in ke iske shi Éakinsa kar in Æara zuwa gareshi id