yara".
"ya dai fi mata kwanciyar hankali".
ni dai ban ce komai ba, ban sani ba yin shiruna ne ya Æular da ita ko mene oho, na dai ga ta fusata ta Æara ruwan bala'i sai faÉin maganganu take na cin mutuncina da zarafina.
Shi da kansa ya shiga bata hakuri, bata dai yi shiru ba ta haÉe faÉan har da shi Éin tana zagi, ya rikice yana dubana rai tamau tare da watsa min mugun kallo ya ce,"wai Sa'ida me yake damunki ne, a gaban mahaifiyata fa kike, kin yi mata laifi kuma ba za ki iya buÉe baki ki bata haÆuri ba, zan Éata miki rai fa".
ido na Éaga na kallesa na sauke, in bada hakuri! akan laifin da banji ba ban gani ba? ai haÆuri na gama bayar da shi a gaban iyayena, sai dai komai zai faru ya faru amma ban bawa kowa haÆuri a cikinsu, da me zan ji?, Cin mutuncinsu da zarafinsu? Ko kuma sharrin yaran da makircinsu?
Æuluwa yay sosai ya shiga jijjiga kai yana nuna ni da yatsa ya ce,"mahaifiyata! kin fi Æarfin bata haÆuri ko Sa'ida, za ki gane kuranki".
Iyam ta ce,"Æyale mahaukaciya marar hankali da tausayin yaro, juyar banza da wofi mara tarbiya da bata san darajar uwa ba, Allah dai ya rabamu da Æyashi da baÆin ciki da girman kai, ki bari randa kika haifa ko iyayenki suka zama wasu kyayi kowanne iskanci, amma yanzu wace ke, juya ko Æ´ar talakawa? kina gida zaune ba ilimi babu aiki, komai sai dai a miki".
zagin ya ci min rai, nayi kamar na miÆe amma na daure na zauna saboda tunawa da iyayena.
faÉan Abbaa da kashedin Kaka gareni ya fara tariya cikin kaina, na hango Éacin ran da ke shimfiÉe saman fuskar mahaifina. kawai sai na gyara zama cikin karyewar zuciya, na fuskanci Iyam cikin raunanniyar muryata na ce,"don Allah don Annabi kiyi haÆuri da dukkan abun da ya faru".
shima na fuskance shi a hankali na ce,"kaima kayi haÆuri".
cikinsu babu wanda yace da ni komai. kaina dai a Æasa duk wanda ya kalleni sai ya ji tausayina. shi kuma ya numfasa ya ce da mahaifiyar tasa,"Yanzu zan kai ki gida ko sai anjima?".
kamar wanda ya tsikareta tayi saurin cewa,"wanne gida kuma Nazifi, ka mance yau Malam ya bar Æasar ne, kai dai Allah yay maka albarka ya Æara buÉi, ko don sanin girman iyaye da kayi ba zaka taÉe ba wallahi. ai zuwa nayi na zauna tare da ku zuwa Baban naku ya dawo, tunda naga lamarin gidan na ka yanzu sai Æalu innalillahi, to kuwa kaga ai gwara a sami babba ya zauna tare da ku ko a samu raguwar wasu iskace iskancen. ni tun wancan karan da ta hora yaran nan da yunwa hankalina ya daina kwanciya gaba Éaya, to yau kuwa da naji batun tana neman sumar da su ai bana ci gaba da zama ba ayi kisan kai muna can nesa, gwara in zo in zauna tare da su ganin idona yasa a rage wata muguntar".
furucinta ya zama daidai da saukar tsawa a tsakiyar kaina, na ambaci innalillahi wani innalaihi rajiun, zaman Iyam a gidan nan? wanne irin zama za'ai kenan? shikenan kuma na Æara shiga gagarumar matsala, farin ciki kam nayi bankwana da shi, sai abin da naji na gani.
"wanne Éakin zan zauna? ko kuwa ma Éaki Éaya zamu tare da yaran, don ni gaskiya ina tsoron sharrin wannan Æ´ar, kar ta koma bin cikin dare ta cutar da jikokina, ba ka san wanne shiri mugun mutum ya ke yi ba, Allah dai ya karya alÆadarinta kawai".
ya sauke numfashi ya ce,"su a sama su ke, ke kuma kinga ba za ki juri hawa da saukar ba, tunda akwai Éakuna a Æasa sai a kimtsa miki wanda kika zaÉa".
ya miÆe yana Éaukar jakar kayanta, suka yi Éakina na Æasa, suna zuwa naji ta ja dogon salati tana faÉin,"Nazifi ya zaka kawo ni wannan Éakin, na san mene a cikinsa zaka ce in kwana, ai wallah sam ba zai yiwu ba. gwara ka barni in ke kwana a falon na ku ni ba baÆuwar zafi ba ce, amma wannan Éaki kuwa sai in Æur'ani aka sauke masa akayi turarukan karya sihiri shine sai in iya kwana, amma ba haka sakaka ba ban yo shirin komai ba duk da cewar azikarin safe da maraice bai wuce ni".
ya ce,"haba Iyam ko baÆo ai ba za'a barsa ya kwana a falo ba balle ke mahaifiyata, Éakin naki ne sai an kaÉe Æura tukunna kin san ba wani amfani ake da su ba, kuma dole sai an sanya gado a ciki".
"ai Nazifi ko a dandariyar Æasa ni mai kwana ce akan dai kwanan Éakin matarka".
"tom bari naje na gyara miki".
su ka dawo falon har lokacin ina zaune yanda suka tafi suka barni, suka wuce zuwa Éakin da zata zauna ta dakatar da shi da cewa,"a'a to wai ita waccan shafaffiya da mai Éin Æ´ar waye da tafi Æarfin zuwa tayi gyaran".
ta juyo gare ni tana cewa,"ashe haka yake tsoronki shiyasa ya kasa Éaukar matakin komai game da rashin haihuwarki. to tashi maza gyara min wancan Éakin na farko a shi zan zauna. in aka ce mutum na da haÆuri sai ai ta cutarsa, yanzu a Æ´aÆ´ana in ba shi da yake da uban haÆuri ba wa zai zauna kallonki kina Æin girmama ni".
haka na miÆe na wuce na shiga Éakin, ni dai tunda muka zo gidan zan ce sau Éaya na taÉa buÉe shi na shiga shima ranar Malam ya bada