NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 55 of 97

a ya suɓuce da faɗin innalillahi wainna ilaihi rajiun, hasbunallahu waniimal wakil, ina fadar hakan kuma naji gabana ya sassauta faɗuwar da yake tare da samun wani guntun kuzari na sauko a gadon kamar mara jini na ƙarasa na buɗe ƙofan. "Iyam ce ta zo, Abban kuma ya fita". na ce mata gani nan zuwa kana na koma ciki na wanko fuskata da sabulu tare da tsayar da kukana. na ɗau mayafin abaya na yafa na fita. jin takun saukata ta kallo bene tana cewa,"kina takaicin zuwana ne da kike wani sakkowa a hankali". maganartata sai naji kaman ta harɗe ni don saura ƙiris in faɗo daga benen. na ƙarasa wajenta cikin sauri ina durƙusawa in ce,"sannu da zuwa, an zo lafiya". banzan kallo ta min tana cewa,"kina ɗaki abinki a kwance har da su rufe ƙofa, kika bar yara komai zai faru da su ya faru da su ba asararki ba ce". cike da ladabi na ce,"da yake ban jima da shiga ɗakin ba ne, tara muka hau saman da su ma suka shiga ɗaki ban san sun sakko ba". taɓe baki tayi tace,"in kana da ƴaƴa ai baka shiga ɗaki ka kulle ka barsu su ɗaya ba, zama kake ka kula da su". a hankali na ce,"ayi haƙuri. ina wuni". bata amsa min ba ta mayar da hankalinta ga jikokinta. na miƙe a sanyaye na shiga kitchen, abincina da mu kai takeway na juye mata na haɗo da drink da ruwa na kawo mata. kallonsu kawai tayi kamar bata gani ba kuma bata ji me nace ba. na zauna a rakuɓe ƙasan carpet tace,"shi Nazifin yayi ina ne haka?". "bara na kirawo shi a waya". ta dakatar da ni,"da tawa wayar ai, ungo kira min shi". hmm dama ko da na hau saman ma wallahi ba kiransa zan yi ba, zan sha zamana ne in sakko in ce mata wayar bata shiga. sai bayan katsewar kiran farko sai ga shi ya kira, na ɗaga na mika mata, suka gaisa take faɗa masa,"na zo ne ai ake cewa baka nan". ban san me yace mata ba naji ta ce,"to shikenan sai ka dawo ɗin, amma ka hanzarta". ita da yaran suke ta hirarsu, ni ba abin in tashi ba na jawa kaina magana, don haka na gyara zamana na jingina da kujera ina salatin Annabi cikin raina. sai da aka yi sallar magriba ya dawo yake bata haƙuri da cewar yaje ne gidan Alhaji Fari. na basu wuri na koma ɗaki bayan wasu mintuna ya kirani a waya ya ce na sakko. da na fito ina jin surutun yaran a ɗakinsu suna musun da suka saba akan assignment. ni da shi duk muka zauna a ƙasa, kamar wata basarakiya sai da ta ja lokaci kafin ta ce,"Sa'ida me yaran nan su ka yi miki ne kike azabtar da su umm?". da ƙwarin gwiwata na ce,"ni ba su yi min komai ba Iyam, kuma abun da zuciyar kowa ke faɗa akan ina zaluntarsu sam ba haka ba ne, sai dai ba me yarda da ni amma Allah na shaidata". wai wannan ƴar maganar da nayi sai ta tunzurata ta kama cewa,"a'a tou ai ba ce nayi ki faɗa min magana ba Malama ƴar gidan Malamai da su kaɗai su ke da Allah. to ni dai batun jikokina ne zan shata miki layi tsakaninki da su, ba sai na rantse miki ba domin ni maganata ko babu rantsuwa tabbatarwa nake na aikata abun da na faɗa, Sa'ida in har kina son zamanki da ɗana to kar ƙara bar min jikoki da yunwa, hakana kar hannunki ya kuma kaiwa jikinsu, ke ɗaga murya ma ban yarda ba. idan wani baƙin ciki ne a ranki kike so ki huce akan wani to ga shashashan mijinki nan ki huce akansa, ki cutar da shi shi ɗaya amma banda jikokina...na san ba komai ke damun ki ba face baƙin ciki da hasssada, yo banda ma dai halin ɗan adam na butulci ba ki haifa masa ba kuma ki ce ba za'a ba shi ba, ke kawai da ke ɗaya zai zauna ba batun wani ya raɓe shi, in da ya so ai aure zai ƙara wata matar ta haifa masa ba ya tsaya karɓar ƴaƴan wasu ba, amma ke saboda ba ki san halacci ba shine za ki ɓige da cutar da yara saboda ki raba tsakaninsa da ƴan uwansa, to ta Allah ba taki ba, ba yanda za'ai yayi ta cika miki ciki da abinci kina kasayarwa a masai, wanne kalar taimako ne baiwa ƴan uwanki ba? ina ce har kasuwa ya kai Yayanki. butulu marar halacci, to yara ne dai jinin Nazifi ne, shi da uwayensu ciki ɗaya suka fito kuma nono ɗaya suka sha, kinga kuwa ba ki isa ki raba shi da yaran nan ba sai dai baƙin ciki yasa ki haɗiyi zuciya ki mutu ruwanki. ni to bara ma na faɗa miki abin da baki sani ba, yanzu sam zamanki tare da shi bana ƙauna wallah, Allah ya gani ƙaunar jin zanceki ma bana yi, kin sire min kin fita a raina, badan kar ace na zama sheɗaniya ba da tuni na yiwa tufkar hanci, yo me amfaninki auren macen da bata haihuwa, zama da juya ai ƙaddararran zama ne, haka kawai ina so naga tsatson Nazifi kin babbake gida kin hana". Haihuwa! Juya! kalmomin nan nasa zuciyata matsewa, dalilin furucinta hawayen da ban san da su ba suka fara sauka. shi kuma ta shiga cewa da shi,"Kai kuma ka ɗauki mataki, ka gargaɗi juyar matarka akan taɓa min jikoki, idan ba zaka iya ba duk kalar matakin da na ɗauka akanta ita ta jiyo". ya ce,"kiyi haƙuri Iyam, ai na mata faɗa kuma tayi alƙawarin zata g
🏠