NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 54 of 97

a na fuskance shi na rissinar da kai na ba shi haƙuri tare da alƙawarin ba zan kuma cutar da yaran ba, ba zan ƙara yi masa wani laifi ba. kuma memakon komai ya lafa sai ma sabon faɗa ya tashi, Abbaa dai bai ce komai ɗin ba bayan maganar da yayi sai Yayyuna da Kaka ne kamar za su cinye ni ɗanya. sai da Abbaa ya buɗi baki yace da Nazifi muna iya tafiya sannan ya miƙe yay gaba, Yaya Imam da Yashaik suka bi shi, ni dai kasa tashi nayi sai lokacin na rarrafa na ƙarasa gaban mahaifiyata wadda ko tarinta banji ba a wurin, na kifa fuskata saman cinyarta, kuka na ke yi sosai a hankali ina faɗa mata ban aikata ba, ba ni ke da laifi ba akan komai, to roƙa min Abba ya sauka akan hukuncin da ya yanke. ta ɗora hannunta a saman kaina, kafin ta kai ga magana Abbaa ya doka min tsawa ya ce,"zaman uban me kike da ba za ki tashi ki bi mijinki ba". da sauri na miƙe jiki duk babu ƙwari ina jin jiri na neman zubar da ni, na saita kaina tare da janyo fuskar hijabina don kar yaran su fahimci abun da ya faru, Ummani ta ruƙo hannuna muka fito daga ɗakin. falonta mu ka shiga muka tsaya a tsaye, a hankali ta ce,"tsakanin ke da mijinki ban san bayan wa zan bi ba, ke da shi duka akwai yardata akanku. amma ni dai ki sani haƙuri yana daga cikin abun da ya ke taya bawa samun nasara a duniya da lahira Sa'ida, duk abun da aka ce babu haƙuri da juriya a cikinsa to zai wuya abun ya kai ga nasara. kwantar da hankalinki ki cigaba da rayuwar ki cike da tawakkali tare da godiya ga Allah, har kullum ina faɗa miki Allah na tare da ke, zai tsaya miki akan lamuranki muddin ba ki da nufin cutar da wani. ke dai riƙe addu'a ki tsarkake zuciyarki ki riƙe yaran da zuciya ɗaya ba cuta babu cutarwa, sannan kar ki ɓata zaman lafiyarki da mijinki, don Allah kar ki ɗauka huɗubar sheɗan ya zuga ki aikata abun da za ki zo kina danasani, yara ne ki gyara musu idan suka yi kuskure na goyi da bayanki domin alhakin tarbiyarsu akanki ya ke, amma ban da cutarwa don Allah Sa'ida, ki ɗaukar min wannan alƙawarin". na so ace na sami wadataccen lokaci tare da mahaifiyata tana lallashina da min nasiha, na samu na amayar mata da abun da ke cikina ko naji salama, amma ina Kaka na fitowa ya kama yi mata faɗa, ita kuma jin wannan da sauri ta sakeni ta ce na tafi saboda bata so sauran mutanen gidan su san abun da ke faruwa. a hanya muna tafiya yay wani ƙasa da murya yacca yaran ba za su ji ba yana min magana a hankali irin ta neman a shirya, don munafurci wai haƙuri ya ke ba ni, yana faɗa min in kwantar da hankali kar in saka damuwa a rai, zai fahimtar da ni idan mu ka koma gida. ni dai banza na yi masa har lokacin kuma idona bai daina zubar da hawaye ba, tsabar neman gindin zama har wani tambayata ya ke wanne restaurant zamu je muci abinci idan mun koma na huta da girki. can kuma sai ce yayi,"kin sanni akan son yara shiyasa amma ba don in muzguna miki hakan ya faru ba". "hmm to waye ba ya son yara? Ba da tarbiya ne kawai ba kowa ya iya ba". "hmmm". ya ce yana kira sunan yaran, su ka amsa yana ce musu,"Antynku ta ce muje restaurant mu ci abinci amma wai wanne kuke so mu je?". caraf tantiriyar cikin na su wato Atika ta ce,"Anty inda muka je last week yafi kyau Anty aje can". jin ban kulata ba ta ratso ta tsakanin kujerunmu tana leƙo kanta wajen fuskata. "kin ji Anty please". sai a sannan na yi murmushin da ya fidda sauti na ce,"tom shikenan yanda ku ke so". "ina kenan?". ya tambaya idonsa a kaina. na ɗaga ido na masa wani kallo na ce,"Calido". "tom shikenan". ya faɗa yana ɗauko glass ya miƙo min,"saka wannan". na san dalilin bani glass ɗin, saboda haka na karɓa ban musa ba na saka, don duk me hankali kallo ɗaya zai min ya san na ci kuka na ƙoshi, haka kuma ina cikin matsananciyar damuwa. a wajen cin abincin ban iya cin komai ba, tagumi kawai nayi idona akan teburin ina tunani kala kala, shi kuma ina jinsa da yaran suna cin abincinsu hankali kwance, komai suka gani su ka ce suna so sai ya ce a kawo musu, ƙarshe dai nawa abincin sai takeaway aka yi min. sai biyar muka koma gida, ni na fara fita a motar, muna shiga ciki ni da yaran muka yi sama, shi kuma yay ɗakinsa na ƙasa, don shi ra'ayinsa bai fiya wani son hawa bene ba, ko da za'ai ginin gidan saboda na ce ina son bene yasa aka yi amma da niyyarsa duk girman gidan ayi flat. ina shiga ɗaki na kulle tare da faɗawa saman gado na yi lamo abun duniya duk ya ishe ni, jina na ke kamar marainiya mara gata, bani da masaniyar dalilin da yasa Allah ya ƙaddaro min wannan lamarin ba, amma ina roƙonsa ya bani ikon cinye jarabawarsa da dukkan iyawata. ina kwance naji ana ƙwanƙwasa ƙofa, nayi banza saboda na riga na saka maƙulli babu damar a shigo, haka kuma ba zan buɗe ba don sam bana son ganin Nazifi da yaran, kusan mintuna ɗaya ana ƙwanƙwasawar sai kuma naji muryar Rumana ta na cewa,"Anty ki fito ga Iyam ta zo". ban san lokacin da bakin
🏠