a Éauko ya buga min a Æashin baya.
"bar ni da Æ´ar banza Nazifi da ina magana zata sako min baki tana Æaryata mijinta saboda ta cika wadda bata san darajan manyanta ba. nasihar me za'a mata bayan ta san daidai da ba daidai ba, to billahillazi Sa'ida ba ki fi Æarfin duka ba a wurina, in kina tunanin ni da kaina ba zan iya lallasaki ba zan sa Imamu yayi miki matsiyacin dukan da za ki dawo hayyacinki. don ubanki ba'a riÆe Éan wani ita uwarki aka riÆeta, ba a haÆuri da halin yaro aka yi haÆuri da na uwarki, wa ya san kalar haÆurin da aka yi da ita, sai ke kin samu yara masu tarbiya da miji na rufin asiri shine za kike cutar da su gaba Éaya".
yay shiru na Æ´an sakanni sannan ya kira sunana da cewar kina jina. na ce "ehh Kaka".
"na rantse da tsarkin mulkin Allah kika janyo abun da zai rabaki da igiyar aurenki idan kin zauna a gidan nan Allah ya Éauki raina a ranar, kuma sai nasa Salman ya sallamaki a Æ´aÆ´ansa. saboda haka ki shiga taitayinki, daga yau kuma wannan lokacin ki aje duk wani rashin mutunci da yake ranki ki kula masa da yaransa, kar na Æara jin Æorafi irin haka, bautar aure kika je yi ba zalunci da rashin mutunci ba".
Na haÉiye yawu da Æyar na ce,"insha Allahu Kaka, insha Allahu kawo Æarata ba zai kuma zuwa gabanka ba, kuma don girman Allah kuyi haÆuri zan gyara nayi alÆawari".
tun Éazu Abbaana bai ce komai ba, kuma naji daÉin hakan domin ban san me nasa Éacin ran zai sa ya gaggaya min ba, duka ne kawai Allah ya riÆi hannunsa darajar aurena, sai kuma takaici abun da Nazifi ya karanta musu akaina ya hanasa magana.
gyaran murya yayi ya kira sunansa sannan ya ce da shi,"Nazifi wanne mataki zuciyarka ke faÉa maka ka Éauka akanta? Kar ka ji nauyinmu".
kansa Æasa ya ce,"Abbaa nasiharku gareta kawai na ke roÆo".
Abbaa ya sauke numfashi ya ce,"Bisa umarnina Nazifi, duk ranar da ta Æara yunÆurin cutar maka da Æ´aÆ´a ko ta nemi ta wulaÆanta Æ´an uwanka don Allah kaima ka wulaÆantata, ka Æuntata mata, ka Éauki duk kalar hukuncin da zuciyarka ta yanke akanta kar ma ka kawota gabanmu...sannan bisa umarnina in har zanci alfarmar zama mahaifi gareka, ina so daga ranar yau ka datse alaÆarta da duk wasu mutane da take mu'amala da su idan ba Æ´an uwanka ba ko nata, na tan ma sai wanda ka yarda tayi mu'amala da su in ba su maka ba ina goyon bayanka ka ci mutuncin duk wadda ka gani cikin gidanka".
sai kuma ya juyo gareni ya ce,"ke kuma ki buÉe kunnuwa da kyau ki jini, idan Æ´aÆ´an Sa'id ko na Imam aka Éauka aka baki haka za ki cutar da su?".
"a'a Abbaa".
"to don me akan Æ´aÆ´an Æ´an uwan mijinki, baku fa akai saboda tausaya muku an san cewa rashin haihuwa da raÉaÉi, amma saboda rashin tausayi da imani sai ki Éige da mugunta da zalunci Sa'ida, kuma akan Æanan yara, haka ake yi dama? silar haka yanzu ba sai ki raba shi da yayunsa ba. yanzu can sun ba ki kin kasa riÆesu, kina tsammani cikin Æ´an uwanki yanzu akwai wanda zai sha'awar Éaukar Éansa ya ba ki? in Allah ya ba ki ki mutu kika barsu wa zai ji tausayinsu ya Éauka tun da an san uwarsu ba mutuniyar kirki ba ce".
ya nunfasa,"to daga yau bisa kashedi me girma kar ki kuskura mijinki ya Æara kawo Æorafi akanki idan ba haka ba za ki shiga uku a hannuna, zan mugun saÉa miki ne, ki cirewa kanki duk wani mugun Æuduri, zuciyarki ki ta so yaran kamar ke kika haifa, yanda ba'aji Æyashin Éauka a baku ba bai kamata ke kiji Æyashin kula da su ba".
"nayi alÆawarin gyarawa Abba, laifina ba zai Æara zuwa gareka ba da yardar Allah, ka yi haÆuri ka yafe min".
na faÉa cikin kuka me taÉa zuciyar me saurare ina haÉa hannayena wuri Éaya alamar roÆo.
ya Éauke ido akaina ya mayar kansa ya ce,"kayi haÆuri Nazifi da duk rashin mutuncinta, na kuma gode da ka kawota muka san halin da kuke ciki. sannan abu na gaba da zan faÉa maka shine; yau ta zama rana ta Æarshe da zan kuma ganin Sa'ida a cikin gidan nan har sai nan da tsawon shekara guda".
ya faÉa yana juyawa ya kalli Yashaik yace,"Sa'id ka rubuta min kwanan watan yau". kana nima ya kalle ni ya ce,"kin ji me nace ai, kar na Æara ganin Æafarki cikin gidan nan har tsawon shekara guda cif, saÉa hakan kuma zai ja miki samun saÉani da ni ki kuma jawa mahaifiyarki shiga matsala".
ya kalli Nazifi yace,"Allah yay maka albarka".
ya ce,"amin Abbaa, na gode Allah ya Æara muku lafiya...amma ayi haÆuri da batun zu...".
"dakata wannan hukunci ne da na riga na yanke, ka riga ka san kaifi Éaya ne ni bana sauka daga maganata. zuwa gidana na haramtawa matarka zuwansa ko da bisa izininka ne, idan tana so ta haÉu da mahaifiyarta su haÉu a wani wajen".
Éakin yay shiru don hatta sautin kukana babu domin nasa hannu na toshe bakina kamar yanda Yashaik ya umarce ni, babu abu mafi ciwo da naji irin hukuncin da Abbaa ya yanke min. haÆuri su ke ta bashi bayan nima sun sak