NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 52 of 97

ya gagara sakko min, sai zuciyata da naji tana wani irin zafi. Allah ɗaya ya san irin baƙin cikin da ke narke a ƙasan zuciyata. na sani a yau kam ba ni da wani gata sai na Allah, ban da ta cewa domin a wannan dogon jawabin nasa babu mai tsayawa ya saurari nawa, za'a yanke hukunci ne kawai da iya abin da ya faɗa. Kaka na kallonsa ya ce,"Yanzu kai haka ka zauna kana haƙurin ƙunsar baƙin cikin yarinya ƙarama, to ai ba shiru za ka yi ba Nazifi, ci gaba da zayyano shika shikan rashin mutuncin da take shuka maka, sam sam cire tausayinta a ranka ka zayyane mana komai, wannan muguwar ai tafi ƙarfin aikata ta'addacin iya haka, maza zayyano min su kaji na san akwai wasu bila adad, kai kenan tsawon shekaru takwas ɗin nan zaman haƙuri ka ke da ita baka taɓa hankaɗo mana ita nan ba an gyara mata zama". ya ce,"Kaka ni dama cuzgunawa yaran shine dai damuwar, zan ɗauki komai banda cutar min da yara da wulaƙanta ƴan uwana, idan har aka saita haka ɗin to komai me sauƙi ne". na ɗaga kai ina kallonsa da maɗaukakin mamaki, Namiji Ƙayar Ruwa, nama rasa wanne irin tunani zan yi akansa, amma komai LOKACI NE na (oum Mumtaz). "Keee". Kaka ya kira sunan nawa a kausashe. gabana ya faɗi, na ɗago kai a sanyaye ina amsawa cikin dashewar murya. "bar sadda kai ƙasa munafuka, idona za ki kalla muguwa wadda taci amanar tarbiyar da iyayenta su ka bata, kuma ki sani ba kiyi mana adalci ba don sam babu koyarwar zalunci a ɗabi'un ahalinmu, karo na farko da naji ina danasanin wani jika nawa". sai kuma ya juya kan Nazifin yana faɗin,"kaima lusarin namiji da ka bari mace ta rainaka har tafi ƙarfin ka hukuntata sai ka kawota gaban iyayenta, ta ya ma za'ai manyan abubuwa na faruwa irin haka ka zuba mata ido". da faɗin haka sai jin saukar kwanon sha nayi kaf akan fuskata, da ya ke na silver ne hakan yasa naji zafi sosai, na rufe ido a razane jikina na rawa, zafin na cikin ratsa jikina sai ga ƙundumemiyar ashariya daga bakin Yaya Imam wanda ya taso a fusace zai sa ƙafa ya hamɓare ni sai shi Nazifin yay saurin dakatar da shi. "kar ka dakar min mata Imam, ban kawota nan dan a ɗora hannu a jikinta ba, na kawota ne domin a nusar da ita daidai". "rabu da ni Nazifi in saukewa azzaluma mara mutunci iskancin da ya ke kanta...". Yaya Imam ɗin ya faɗa a zafafe cikin hasala. yana shiru Yashaik ya ce,"da ya ke butulu ce ke wadda bata san alkhairi ba, har a ɗauki ƴaƴa a baku abun da ba kowa zai iya ba, ko mu nan ƴan uwanki bamu yi tunanin hakan ba amma ki kasa godiya garesu da ubangijin da ya ba ki ta wata hanyar, sai rama khairi da sharri? to zatonki za ki ga daidai a rayuwa?". Yaya Imam dai so kawai yake ya dake ni, don kaɗa ƙafa yake ta aikin yi yana dunƙule hannu ya yarfar. "banza kawai, duk irin halaccin da mutumin nan yay miki shashasha idonki ya ƙeƙashe saboda kina da baƙar zuciya za ki saka yara a gaba kina cutarwa". Yashaik ya amshe,"yo ina ta san zafin rainon ciki da haife shi da zata san darajar ɗa, tunda Allah bai bata ba ai bari ta kassara na wasu saboda tana baƙin ciki, to kuwa ina za'a ba ki haihuwa Sa'ida a wannan matacciyar zuciyar ta ki, ai ubangiji ma kyawun zuciyar mutum ya ke kallo yay masa ni'ima. ni wallah ban taɓa tunanin ba ki da hankali da tunani ba sai yau, ashe daƙiƙiya ce ke me amfani da ƙwaƙwalwar jahilan farko". ya numfasa saboda yacca amon muryasa ya tsananta nuna ɓacin ransa, ni kuma sai lokacin hawaye yay nasarar sauka daga idona, na ɗora hannu bisa goshina kaina kife ƙasa ina jin wani azaba daga zuciyata tamkar an cirota ana babbakata, ai dama ni na san kam yau sai abinda naji na gani, haka ahalina su ke idan ransu ya ɓaci komai faɗa maka su ke yi, don ma dai shi ɗin ya hana a dukeni da ba za su tsaya doguwar magana haka ba, kawo yanzu ina nan da fasashshen jiki. zan buɗi baki nayi magana Kaka ya dakatar da ni a tsawace,"kika yi magana a wurin nan sai na faffasa miki baki don uwarki da ubanki mara mutunci. idan auren kika gaji da shi yasa kika tsiri wannan iskancin yanzu zansa ya sake ki ya huta da masifa, daga nan sai inga a inda za ki zauna kiyi zaman zawarcin don ba'a gidan nan ba". ya kalli Nazifin ya ce,"maza rattaba mata kalaman da za su rabaka da ita har abada, in ya so kaje ka auro mai mutunci da tarbiya da ilimi me imani a zuciya ka zauna da ita wadda zata riƙe maka yaranka tsakani da Allah. ni bana goyon bayan kaci gaba da zama da wannan ƴar banzar yarinyar, ba sonka take ba, gwara ka sakota ko bara ne ta koma yi don babu wanda zai kuma ɗaura mata aure, ba mutanen banza ba ne mu da zata je ta wulaƙanta mana ahali, uban da yake zugata taje taci gaba da zama da shi". kuka na fashe da shi sosai ina girgiza kai na ce,"Kaka wallahi duk ba haka ba ne, ba haka ba ne Ka...". Nazifin yay caraf ya ce,"Kaka ayi haƙuri ai mata nasiha kawai...". sandar da Kaka ke doragawa wani lokacin ita y
🏠