allo ya watsa min ba tare da ya amsa ba, yaran suka gaishe shi yana musu fara'a ya amsa tare da kama hannunsu suka shiga gidan, bayan yace da Hubbi Bismillah ka shigo.
ya dube ni ya ce,"muje".
na yi gaba yana biye ni da ni a baya, jikina duk a sanyaye don ban san me ke faruwa ba, kuma ÆwaÆwalwata ta kasa haska min abin da ka iya faruwa Éin.
Ummani na tsakar gida muka shiga, yanayin fuskarta sak na Yashaik babu annuri, karo na farko da banga farin cikin ganina ba duk sanda na zo gida a tare da ita. ta sakarwa Hubbi fuska su ka gaisa tana shi masa albarka sannan ta ce mu shiga falon Kaka.
shi ya fara shiga daga ciki, ni kuwa tsayawa ni na kasa shiga saboda tsabar tsoro, Æirjina sai fat fat ya ke, Ummani ta zo ta wuce ni ta shiga. Kaka ya danno min zagi ba shiri na Éaga labule na faÉa ciki.
ciki ciki duk suka amsa gaisuwata, Kaka ne da Abbaa da Yashaik da Yaya Imam sai Ummani, banga yaran ba ina ga suna Éakin Ummani.
gefen kujerar da Ummani ke kai na zauna, a tsawace Kaka ya ce in dawo daga tsakiya, na miÆe Æafafu na rawa na isa in da ya nuna min.
Kaka ne yay gyaran murya yana fuskantar Hubbi ya ce da shi,"Nazifi me yake faruwa? ka faÉi duk irin Éibar albarkar da Æ´ar banzan yarinyar nan ke yi maka a gidanka ni kuma zan sa ka Éauki matakin da ya da ce da ita don ubanta Salman da yake zaune kusa da ni, ahalinmu kaf ai babu Éan iska to me kuma dalilin da zai sa a samu Æ´ar banza a gidan aure".
furucin na Kaka yasa na Éago a ruÉe ina kallonsa, kafin in kalli Hubbi da ya fara rattabo zance tamkar Éan jarida.
"amm Kaka dama matsalar dai akan yaran da Yayyuna su ka bani ne saboda sunga Allah bai azurtani da haihuwa ba, wannan tausayin yasa suka Éebi yara har biyu suka bani halak malak, sun bani domin suna da yaÆinin zan riÆe su bisa gaskiya da amana haka kuma da yaÆinin ita iyalina zata kula da su. da lafiya lafiya mu ke zaune da Sa'ida Kaka ba wata matsala sai Éan saÉani na wani lokaci da ba'a rasawa ga ma'aurata. amma tun zuwan yaran sai ta sauya gaba Éaya, ta canja Éabi'u, ta Éauko wasu halaye na banza ta Éorama kanta, ban san wa yake zugata ba ta Éora karan tsanarta akan yaran nan, bata sonsu sam, kuma abin sai ya shafa har da ni, yanzu haka zancen da na ke tsakaninta da Yayyuna kallo ne bata ko gaishe su.
kuma da aka ce an mallaka min yaran saboda na fita hakkinta don ban san ba ko ita zata iya cutuwa tun da ba kowa ne ke iya karÉan Éan wani ba, lokacin ta nuna farin cikinta har da hawayen murna. amma yanzu ban san mene matsalarta da yaran ba, tsakani da Allah suna mata biyayya, amma ita kenan kullu yaumin cikin muzguna musu take yi, bata da burin da ya wuce taga sun Æuntata, tamkar marayu haka suke komawa a gidan idan ba nan.
kwanakin baya haka ta hora su da yunwa, ta hana su abincin safe kuma ta Æi ba su na makaranta, wallahi Éayar cikinsu Atika daga makaranta aka kaita asibiti kamar zata mutu saboda ciwon ciki, sai kirana akayi a waya aka shaida min, ina zuwa asibiti likitan yace yunwa ce a dinÆa bata abinci.
to wannan ya wuce ma. jiya nayi tafiya kaduna tasa yaran a gaba ta zane akan ta dafa abinda ba sa ci sun ce a dafa musu wani, kawai sai ta hau zaginsu har tana cewa zata saka su wani gida a saka su a Éakin karnuka, wai har da baÆinta suma suka rufarwa yaran, haka su ka yini babu abinci sai da safen nan da zan kai su makaranta su ke faÉa min abin da ya faru, saboda a gidan kasa faÉa min suka yi saboda tsoronta ta ce zata faffasa musu baki. wallahi yanzu haka shatin waya ne a bayan ita Atikar alamar ta zanu iya zanuwa, sai da ta nuna min ma na ke jin zazzaÉi a jikinta alamun ba lafiya tabbacin dukan ne ya haifar mata da zazzaÉi, har raina ban ji daÉi ba, ina son yaran, ko Éan wani ba zan so inga ana zaluntarsa ba wallahi balle wanda ya ke nawa, duk da bani na haifesu ba amma ko yau Allah ya bani nawa ba zan banbanta su ba.
tsakani da Allah idan iyayensu suka san abinda yake faruwa sai ta raba zumuncina da su, abin da ya faru wancan karan har yau mahaifiyata na fushi da ni, ba wanda zai ji daÉi yaga ana cutar masa da Éa.
to Kaka ni tunda gaskiya na kasa gane kanta shi ne na ce bari na kawota gareku, aji ta bakinta mene yaran su ka mata, kuma mene matsalarta da su Æ´an uwana da yanzu ma gaba Éaya bata shiga sabgarsu don ko abu ne ya kama na gidanmu kaitsaye zata ce min ita bata son zuwa. to ayi haÆuri a mata nasiha ta gyara don ni idan nayi mata ta dinÆa botsare botsare a gidan, in kuma wani laifi na mata da yasa ta Æullace ni ta faÉa a samu masalaha. amma gaskiya tsakani da Allah Kaka zan faÉa muku akan Æ´an uwana ko Éan da na haifa a cikina zan iya rabuwa da shi, haka akan yarana zan iya rabuwa da uwarsu ma muddin ta takura musu. ta faÉa idan ba zata iya karÉar yaran ba ne to".
tun fara jawabinsa na zama tamkar matacciya, da Æyar na ke iya fidda numfashi, hawaye kuwa tsabar ruÉani da mamaki gami da baÆin ciki