NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 50 of 97

haka ba bakinki zan fasa ba gidan su Siyama zan kai ki a saki a ɗakin karnuka su cinye ki". ai ko ta tsorata sosai da furucin nawa, don haka ta shiga roƙona in yi haƙuri ba zata sake ba. na juyar da ita ta fuskanci Maman Yasmin, yanda nayi maganan a tsawace yasa bakinta na rawa ta furta. "kiyi haƙuri ba zan ƙara ba".. na ƙara firgitata ina cewa,"haka ake bada haƙuri, tsuguna ki ce don Allah". jikinta na rawa ta tsuguna gaban Maman Yasmin tana cewa,"Anty kiyi haƙuri don Allah, ba zan sake ba wallahi, ki roƙi Anty ta sakar min kunnena". kashedi na yi mata me kyau kafin na ce ta kwashe biredin da ta zubar ta cusa haka nan taci, haka ta zauna ƙasan tayels tana ci tana kuka, kuma tana gamawa na ce ta tashi a kusa da mu ta tafi ɗaki ta zauna, kuma da kaina zan kaita islamiya in faɗawa Ya Ustaz abin da tayi. ai fa nan hankalinta ya daɗa tashi tai ta ƙara bani haƙuri. ko da su ka shirya tafiya islamiya sai da ta zo har gabana ta duƙa ta ƙara bani haƙuri kar naje islamiya na faɗawa Ya Uztaz in ba haka ba a mari zai sakata. sai da tayi min alƙawarin ta daina tukunna na ce shikenan su tafi makaranta kuma ayi karatu da yawa. sai bayan tafiyarsu Hindatu ta ce,"cabɗijam! Sa'ida haka kike zaune da yaran nan dama? anata miki murnar samun ƴaƴa ashe ke kina nan kina fama da halin su. to ke kuwa me zai hana ki mayarwa da iyayensu ki ce kin yafe". guntun murmushi nayi na ce,"Hindatu kenan to ai bani aka bawa ba ko". "cabɗi to sannu danga uwar haƙuri. ai wallahi da ni ce tuni labari ya daɗe da sauyawa. don wallahi tallahi ba zan ɗauki ƴaƴa marasa mutunci irin wannan ba sai dai in kuwa ya auro wata ta ɗauka, rashin haihuwar hauka ne da za'a ɗauko masifa a dire miki, wannan yarinyar dai a felle take don da gani zata yi makirci". Maman Yasmin ta numfasa tana cewa,"sun raina wanda ya alaƙantu da ke ina ga ke kanki? Sa'ida haƙurinki yayi yawa gaskiya, na san ba akan ƴaƴan kaɗai kike fuskantar ƙalubale ba harda iyayensu ma, don ina da tabbacin iyayensu su ka basu lasisin cin mutuncinki, in ba haka ba ina wannan ƴar zata san wani juya, kar ki mu sa min domin kin san ina da ilimin karantar yanayin mutum zaman haƙuri kawai haƙurin cutar da kai. don haka ina mai ba ki shawara tun yaran nan ba su girma sun fi ƙarfinki a cikin gidan nan ba ki amso abinda yake na ki, in ba haka kuwa kina ji kina gani Allah sai sun iya rabaki da mijinki. yo da irin ƴaƴan nan ai gwara kishiya, su kansu ƴan uwan na sa ki buɗe musu ido". haka Maman Yasmin da Hindatu su ka sanya ni gaba da faɗan sanyina yay yawa, ni dai jinsu kawai na ke yi ina binsu da uhmm in sun ce ga shawara kaza da kaza, abu da na san na ɗauka a cikin maganganunsu shi ne takawa yaran burki akan rashin mutuncinsu, don idan ba haka ba zasu raba ni da mutane, tun da ba kowa za su yiwa rashin kunya ba yay sha'awar ƙara zuwa gidana, kuma su ɗore a haka duniya ta ɗora laifin akaina ace saboda ba nawa ƴaƴan ba ne yasa ban basu tarbiya ba. na samu ma da ƙyar na kashe maganar, sai bayan la'asar kafin su tafi. sai dai fa Hindatu kamar za tayi bindiga saboda haushi da takaicina, wai haƙurina ya wuce ƙa'ida. washe gari da safe bayan Hubbi ya kai yaran makaranta ya dawo, mu ka yi breakfast sai dai tun dawowarsa naga kaman akwai matsala, don ba haka ya fita ba, na tambaye shi bai ce min komai ba, na ce Allah ya kyauta don bana so na takura masa da tabaya ya fusata, yana daga cikin mutanen da in ransu ya ɓaci to basa so kowa yay musu magana sai sun sakko, ban kawo matsalar tsakanina da shi ba don na san babu abin da ya haɗamu, lafiya lau ya fita kai su makaranta har yana tsokana ma wai na fara tumbi. da rana bayan ya ɗauko yaran a makaranta, na zuba musu abinci suka ci, na ce musu zanje in kwanta in huta idan lokacin islamiya yayi su shirya su wuce. shigata ɗaki ba daɗewa sai ga Atika ta shigo ɗakin tana faɗin,"wai ki zo inji Abba". bayanta na bi, ina shiga ɗakin kamin nayi yunƙurin magana ya ce,"sako hijabinki zamu fita". yanayin yanda yay maganar kaɗai ya shaida min bafa lafiya, na fita a ɗakin kafin na sauko har sun kai mota shi da yaran, can na tarar da su ina zuwa na buɗe na shiga. magana na ke ta masa tun barowarmu gida bai ce min ƙala ba, raina ya ɓaci zuciyata ta ƙuntata, don bana so ya ke min irin haka a gaban yaran, shiru nayi ban ƙara magana ba har sanda na ɗago ido naga yay parking motar a ƙofar gidanmu. nan kuma naji yana waya yana cewa,"Yashaik mun ƙaraso". ya sauke wayar a kunne yana juyawa ya kalli yaran ya ce,"ku buɗe ku fita". sai bayan sun fita nima ya ce da ni,"fita mu je". na ce,"wai lafiya?". "za ki gani in mun shiga daga ciki". da tarin tambayoyi fal a raina dangane da zuwanmu gidan na fito daga motar, fitowata tayi daidai da isowar Yashaik, su ka yi musabaha nima ina cewa,"Yashaik ina wuni". wani wawan k
🏠