ncan zuwan da nayi na Æarshe babu wata tarba mai kyau daga uwar mijina, jin haushina tsantsa bayyane a saman fuskarta, don ko da na gaida ita da Æyar ta amsa mini, sona kam dai yanzu ba shi a tare da ita. zama da nayi a Éakinta ma sai ce tayi da in fita daga parlo ko wajen Amarya tana so zata huta. haka na kwaso jiki na fito parlo in da anan na sami Æ´an mata gidan suna kallo ana hira, Rumana da Atika na ganina amma yaran nan babu wacce ta gaida ni kamar ma ba su sanni ba, Atika ma da nayi mata magana sai tsaki ta min tayi wucewarta Éakin Iyam, abin ya taÉa zuciyata sai naji ina ma kar su koma gidan namu don gani nake komawarsu zai Æara taÉarÉara zamana da Hubbi.
yini muka yi a gidan, da Amarya muka ta hira duk ta Éebe min kewa, dama ita Ummaa ba wani sakin fuska take ba, Lubabatu kuwa dama ta gidana ce, in muna tare sai ka ce Hassana da Hussaina, na samu na saki jiki daga takurewar da nayi, don duk na damu da rashin nuna halin ko in kula na uwar mijina, ban san me na mata ba na kuma rasa ta hanyar da zan bi na gyara alaÆarmu.
sai dare ya zo Éaukarmu da yaran, kuma tun a mota yay musu faÉa sosai, faÉa irin na uba da Æ´aÆ´ansa, yace in har suna so su shirya da shi to su girmama ni kamar yanda za su girmama Yaya da Anty Aisha, don yanzu ni ce matsayin uwa a gare su kamar yanda shima ya koma uba a garesu.
to tun daga wannan ranar kam sai dai in ce Alhamdulillah. sati biyu tsakani ina zaune a parlo muna waya da Hubbi, sai ga su Maman Yasmin sun zo, nayi tsallen murna na tafi na rungume su, naji daÉin ganin su sosai, yau dai Hindatu ta wanke laifinta na rashin zuwar min da take yi, a hakan ma ashe da Æyar Babanmu ya barsu su ka zo, wai yana tambayar me za su je suyi min a gida bayan ba jimawa na zo gidan suka ganni.
tare da Hindatu da Sauda mu ka shiga kitchen, dama ban Éora abinci ba da yake Hubbi ya tafi Kaduna yau, kuma sai dare zai dawo, shiyasa ban wani Éora girki ba na ce idan yaran sun dawo a makaranta na dafa mana indomie.
gidanmu mayun taliyar hausa ne da manja da yaji, ko a gida idan za'a dafata haka mu ke haÉuwa da Æ´an Éangarenmu da ƳaÆ´an Babanmu, dama ƳaÆ´an Baba Tijjani tsakaninmu da su kallo, gwara ma Surayya ta kan shigo cikinmu bata da mugun hali irin na Æ´an uwanta. taliyar na bayar aka siyo mana muka dafa tun da naji suna murna a dafa Éin, Sauda ta haÉa mana lemun tsamiya don Maman Yasmin mayyarsa ce.
muna cikin cin abinci sai ga Rumana sun dawo daga makaranta, ba don mun haÉa ido da su ba ba za su gaida Æ´an uwana ba, gaisuwa na Éaya daga abin da basa so, don ko ni da muke kwana tare mu tashi tare ba kullum su ke gaishe ni ba sai dai Abban na su, nayi iyakar yina akan su Éoru akan hanyar hakan amma lamarin na su sai adu'a.
na ce suje su cire kayansu suyi wanka su zo su ci abinci kafin lokacin islamiya yayi, Yasmin sarkin son yara Æ´an uwanta nan fa daÉi ya cikata da ganinsu, duk da sun girmeta don ita shekara bakwai take yanzu. muna ta hirar saurayin Hindatu da zai kawo kuÉi Maman Yasmin na mata tsiya akansa, sai ga su sun sakko, idan na gansu fes fes raina yana sanyi da hakan, sai in Æara jin sonsu sosai, don wallahi ko fushi na ke yi na gansu Éacin raina kan gushe duk da dai ga yanda mu ke da su, ba su Éauke ni uwa ba kamar yanda ni na Éauke su tamkar Æ´aÆ´an cikina.
Rumana ta zo ta zauna kusa da ni tana faÉin,"Anty abinci fa".
kafin nayi magana Atika ta ce,"Anty wai wannan taliyar hausar aka dafa?".
ta faÉa tana nuna taliyar da ke cikin bowl Maman Yasmin na bawa Irfan.
na ce mata,"ehh ita na dafa har ma da salad, in kika ci kunnenki sai ya kusa tsinkewa".
na faÉi hakan ina buÉe cooler sai ce tayi. "ni ba zan ci wannan taliyar ba gaskiya".
ina kallonta na ce,"to me kike son ci?".
"a dafa mana wani abun, soyayyan biredi da Æwai zan ci".
ajiyar zuciya na sauke, bana tunanin ko Éan da na haifa zai juyani kamar yanda su ke juyani, ina binsu ne a yanda suke so ba don komai ba sai don in zauna lafiya a gidan aurena. Rumana da tace zata ci na zuba mata nata suka koma gefe ita da Yasmin wacca ta ce zata Æara. ita kuma na tashi na shiga kitchen na soyo mata biredin na kawo mata, yarinyar nan tun da na bata ta karÉa sai ta tsaya kallonsa tana aikin Éata rai alamun bai yi mata ba.
raina ya Éaci na Éaga mata murya da cewa,"ba za ki wuce kije kici ba sai anjima ki zo kina min kukan yunwa. idan shima kuma ba za ki ci ba sai ki kai ki ajiye don ba zan kuma dafa miki wani abun ba ai na faÉa miki ku dinÆa cin abin da ya samu".
daga mata wannan maganar sai ta saka kuka kamar wacca nasa hannu na buga. nayi mata banza na wuce na barta, Maman Yasmin na kiranta akan ta zo amma ko kallonta bata yi ba, Hindatu kuwa lallashin duniya ba wanda bata mata ba har tana tambayarta me take so amma bata tanka ba, dama zuciyar bala'i ce da ita.
Æarshe kawai sai ta yar da plate Éin, da yake na tangaran ne take ya fashe, ta tu