numfashin mutum a jikina, nayi saurin buÉe ido zan miÆe ya janyoni jikinsa ya rungume.
"kiyi haÆuri da abin da ya faru, Éacin rai ne. kuma kin san ina da son yara sosai ba zan jure ganin wani abun ya samesu ba, hakan shine ya tashi hankalina har ya kai ga abin da na aikata miki. Amma kiyi haÆuri ba za'a sake ba in sha Allah".
hawaye na fara tunawa da irin horon yunwar da yayi min da kalamai marasa daÉin da ya faÉa min, to ni in laifukansa gare ni ma ai sunyi yawan da ba za su Æirgu ba, ga laifin su Yaya amma a haka ya sallame ni zuwa gida ba tare da yi min uzuri ba.
jin hawayena na jiÆa jikinsa sai ya Æara rungume ni sosai yana faÉin,"na san nayi laifi babba kiyi haÆuri ki yafe min Habibty don Allah."
Allah sarki zuciya da abin da take so, hakana tsakanin mata da miji sai Allah, roÆona da yake tayi domin Allah sai naji na nemi laifinsa gare ni na rasa.
na kewaye shi nima ina cewa,"Ya wuce Hubbi. Amma dan Allah ko dan gaba ka dinÆa tsayawa ka fahimce ni kafin Éaukar mataki....".
ya dakatar da ni,"shiii hakan ma ba zai sake faruwa ba fa, duk wani saÉani a tsakaninmu ya zo Æarshe".
haka muka jima rungume muna jin Éumin jikin juna da bugun zuciyoyinmu, kafin ya Éago kaina ya kalli idona ya ce,"Habibty kina jina?."
na Éaga kai alamun eh yace,"nayi kewarki sosai ba kaÉan ba".
a sanyaye na ce,"Nima nayi kewarka Hubbi." na faÉa muryata na neman karyewa.
Yayi murmushi yana ta kallona yace,"Habibty na tambaye ki?."
Na Éaga kai alamun eh yace,"Akwai wani abu wanda aka ba ki kina sha ne na gyara jikinki..? Ina nufin na gyaranku na mata."
Kallonsa nake yi ban ce komai ba hakan ya saka yace,"in akwai ki daina sha ya canja min ke gabaÉaya, bana jin ki kamar da. ba gyara yake miki ba Éatawa yake."
ido na sunkuyar Æasa, lallai namiji, wato sai yanzu lokacin faÉa min gyarana yayi, a yanzu da zanyi amfani kenan.
"Habibty kin jini ba ke ci komai ba".
Na ce,"to Allah ya gyara amma ni dai babu wani abu da na ke sha, asalin ÉanÉano na daka sani shi ne dai ban sha abin da zai Æara min ba balle har ta kai ga ya rage min, amma karka damu zan koma mai daÉin da kake so".
nayi furucin domin na daina Æullewar kai, na cire kaina a sahun matan da ke jin kunyar mazajensu ta fannin soyayya.
Yayi murmushi yaja kumatuna yace,"yauwa Habibty nah".
zameni yay a jikinsa yana cewa,"bara na rufo Æofan falo".
ya faÉa yana ficewa na bishi da kallo. Yana fita nayi saurin Éauko maganin da Maman Yasmin ta bani na fara sha nan take sai da na shanye haÉin zumar tasss, harda goro ma da akace naci rabi amma haka na cinye guda. na leÆa falon naga baya nan nayi sauri na shiga kitchen na buÉe fridge na Éauki ruwan rake da ke cikin jarka na zuba garin maganin, na kafa kai shima na shanye sannan na tsaya sauke numfashi ina zare ido don duk Æarfin hali nayi wajen shan su.
ni tun aurena ban san shan wani abu maganin mata ba, ko lokacin aurena in aka bani bana sha, saboda gab da aurenmu da kansa ya ce don Allah kar in sha komai na gyara da za'a bani, in ke ba shi yana ajiyewa akwai dalilinsa na faÉin hakan. to kuma bayan auren sai ya ce dama yana so ya ÉanÉani asalin zaÆin halittata yaji, to kuma iya wannan daÉin ma ya ishe shi ba sai na Æara da komai ba, kar in zo ina sha in canja daÉi kuma, saboda haka duk ya tattaro wanda ya ajiye da wanda nima na ajiye muka zubar.
to yanzu tun da anzo lokacin da asalin halittar tawa ya bar masa daÉi ai sai in kama kaina inyi abin da ya dace ba in zauna da sakakkun laÉÉa ba. har zan fita a kitchen Éin idona ya kai kan fruit na Éauka nasha nasha na bar na bari, don bana taÉa mance wata likita da ta faÉa min cewa babu mafi muhimmanci a gyaran jikin mace irin shan kayan marmari, kuma sosai da na lazumci shansu na ga sakamako mai kyau.
ni ko a yanzu ma ban wani yarda da dalilinsa ba, kawai dai ya faÉa ne don kare kai ya kuma wanke laifinsa.
ina shiga na tarar bai dawo Éakin ba, don haka na shiga tuÉe kayana na Éauki towel na Éaura. lokacin ne kuma ya shigo sanye da kayan bacci masu taushi yana ta Æamshinsa me daÉi.
muka haÉa ido da shi na wuce ina zuba kayan da na cire cikin basket. zan wuce shi ya ruÆoni yana faÉin,"ina baccin?".
da muryar shagwaÉa nace masa,"na kasa, wanka na ke so nayi tukunna".
na Æwace hannuna nayi toilet Éin sai dai ina zuwa bakin Æofar sai na dakata na waigo na kalle shi na ce,"Hubbi kai ba zaka yi ba?".
"daga wanka na fito ai".
na narke idanu ina langwaÉar da kai na ce,"to ka zo kayi min, ni duk na gaji".
murmushi yay wanda na rabon da naga irinsa a fuskarsa zan rantse an shekara. ya cire rigar jikinsa ya naÉe wandon ya kama hannuna muka shiga banÉakin.
Tare mu kayi wankan da shi, kuma tun a banÉakin labari ya fara canjawa, ko da muka fito tuni na kasa daurewa salonsa, ni dai sai in ce rabon da mu mu'amalantu irin t