NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 44 of 97

n yayi wanda yake ɗauke da hotonsa da nata, hoton tun na ɗaurin aurensu ne, kuma agogon Yaya ce ta basu gudunmawarsa. ƙarfe huɗu da rabi na yamma, ya sauke numfashi ya rumtse ido gam tare da riƙe kansa, anya yau zai iya kwana shi ɗaya a gidan nan? anya zai iya kwana a koma ina ne babu motsin Sa'ida? miƙewa yay tamkar wanda aka tsikara yana isa gaban TV ya kashe, sannan ya dawo ya ɗauki maƙullan mota ya fita ba tare da tunanin ina za shi ba, shi dai kawai zai fita ɗin ne don neman mafitar da zuciyarsa ta bashi. ******** na fito daga wanka na saka kaya, ina tsaye na kasa fita sai saƙa da warwara na ke yi, Sauda ta shigo ɗakin tana cewa,"wai ba ki shirya ba? kin san fa yacca abin hawa yake ga shi har biyar da rabi saura, kar muna bakin titi su Abbaa su dawo mu sha faɗa, naga kamar ma ba ki son tafiyar". ba tare da ta lura ba na share hawayena, a sanyaye ina murmushin dole nace mata,"ke kin raina gida ne, ni in da za'a barni ma ai shekara zanyi". tana dariya ta ce,"cabɗi abinda ba zai yiwu ba kenan. bara na ɗauko mayafina". ta faɗa tana juyawa ta fita. daga tsakar gida na jiyo hayaniyar su Walida, ko me su ke wa murna oho ina dai jiyo su sama sama da Ummani. gyalena na ɗauko na yafa daidai kuma da ɗaga labulen ɗakin da Ummani tayi tana shigowa ciki. "kin gama shirin?". "ehh na gama, a samo almajirai su fitar min da su kin san waɗancan marasa kunyar ba taya ni za su yi ba". ina nufin su Asad da Khaleel ƴaƴan wurin Baba Tijjani. tana ta kallona ta ce,"sai kuma ga mijinki ya zo ɗaukar ki". Da mamaki na kalleta nace,"Mijin wa?." ta ce,"mijinki mana, ga shi can a waje yana jiranki. ya jido kayan zaƙi ya bawa yara har da kuɗi, Walida dai ta ce cewa yay ta zo ta kamo hannunki ta kai ki zai bar mata motarsa". da wani mamakin ƙarara a fuskata na sake cewa,"Wai da gaske Ummani?". "A'a da wasa. Malama je ki dawo ki kwashi kayanki ki wuce ki tafi gidanki lada ya isa". "Ummani yaran nan ƙarya su ke yi fa, a halin nan dai Nazifi bai zuwa gidan nan balle har ya ce ɗaukana ya zo yi". "to ai sai kije ki duba idan ba shi ɗin ba ne shikenan, idan shi ne kuma sai kiyi murna". ta faɗa tana fita. ta barni da bin ta da kallo zuciyata na harbawa cike da mamaki gami da tsoron zuwansa. mayafin na mayar na ɗauki Hijabi na saka na fita jiki a mace. Yana zaune cikin mota ya hango fitowarta, ya sauke numfashi ji yake kamar an cike masa wani gurbin da ya jima da yin rami a cikin zuciyarsa, a hankali yake ganin takunta zuciyarsa na motsawa, sam ya kasa ɗauke ido daga kanta domin kuwa gani yayi kamar an canja ta, kwana nawa dudu bai ganta ba amma har ta isa ƙara yin kyau da cika haka?, wato ita hankalinta kwance yake ma, shi yana can rashinta a gidan da matsalar da yake ciki sun hana shi sakat. ko da isa gaban motar sai na tsaya, ina iya jin kallonsa a jikina, fuskar nan tawa naci kunu ina kalle kallen gefe abuna sai ƙifta idanu na ke, yay horn wanda ya ke shaida min na in shigo motar amma sai nayi biris. sai ga shi ya fito da kansa ya taho har inda na ke, yay tsaye gabana hannayensa naɗe a ƙirji. na ɗan ja da baya ina ce wa,"salamu alaikum". sautin murmushinsa na ji kana ya ce,"yi haƙuri Ya Sayyada, amsawar sallama ne dole ba yinta ba". na ce,"haka ne. Abbaan ba ya nan bai dawo daga kasuwa ba. amma Yashaik yana gidansa, in kuma kana iya jiran dawowar mahaifin nawa to tabarma ce da mu". ina faɗin haka na juya zan koma gida ya ruƙo hannuna. "wurinki na zo ba wurin Abbaa ko Yashaik ba". nayi shiru ban ce komai ba. ya faki idon mutane yasa hannu ya ɗago fuskata, na kulle ido ina kauda kai gefe. cikin dakiyata na ce,"wacece ni da na isa ka zo wurina?". "matata". nayi guntun murmushi na takaici ina cewa,"ina wuni". na furta a sanyaye ba tare da na kalle shi ba. ya amsa,"lafiya lau, na sameki lafiya". nayi shiru. ya sake cewa,"zuwa nayi mu tafi". nan ma nayi shiru. ɗumin iskar bakinsa da ya fesar ya sauka a fuskata. ya ƙara faɗin,"ki shiga ki ɗauko kayanki mu tafi". kamar da dutse dai yake magana. ya daɗa ce wa"Habibty Hubbi fa ke magana". nan ma na masa shiru. sai ya sauke dogon numfashi alamun ya ƙosa kana ya ƙara cewa,"ki shiga ki ɗauko kayanki mu tafi, duk abin da za'ai ma yi shi a can gida". nayi masa wani kallo na ce,"ba ni da wani gida da ya wuce wannan". na faɗa ina masa nuni da gidanmu. "kana iya jiran mahaifina ya dawo ka sanar masa ka zo mayar da ni ne. kuma bari kaji zan koma cikin gidanmu amma ba don in ɗauko kaya in bika mu koma wancan prison ɗin ba, ba zan koma in da ban da wata daraja ba". "Habibty mu mance faruwar komai anan. ni ba zan iya tsayawa inga Abbaa ba domin ina jin kunyarsa akan abin da ya faru, kiyi haƙuri ki zo mu tafi kinji". hmm wato tunaninsa ansan turoni gida yay, tsaki kawai bar masa na shige gida. Ummani bata san da dawowata ba saboda tana ɗaki, sai bayan kusan minti goma
🏠