NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 42 of 97

ba akan batu. aifa kamar na turata faɗa take yi har sai da na fara hawaye, don idan akwai abin da na tsana bai wuci ɓacin ran mahaifiyata ba musamman ace ni ce sila. ni dai ina ga tun da ta haife ni ban taɓa shan faɗa a wurinta ba irin yau, haƙurina ba shi yasa ta haƙura ba sai don karan kanta. "ni dama tun ranar da kika zo na kalle ki na kasa yarda da yanayinki, shiru kawai nayi miki. don haka buɗe ba ki ki faɗa min haƙiƙanin matsalar da ke faruwa har kike ikirarin a sakeki ki huta". ina kuka na ce,"Ummani babu komai, kawai ji nayi na gaji da zaman auren, gaba ɗaya na daina farin ciki sai tarin damuwa, maimakon dariya kullum cikin kuka na ke, ni har son Nazifin ma na daina, kuma ban san dalili ba". "ehh lalataccen lamarin babba ne tun da har da kanki yau kike buɗar baki ki faɗi sunan mijinki gatsal abinda ba ki taɓa ba, auren ma kin gaji da shi la gaira wala dalil, to ko dai aljanu sun shigeki bamu sani ba Sa'ida". "aljanu kuma Ummani!". "to in ba aljanu ba haka kawai ki ce kin gaji da gidan aure kin daina son miji duk babu dalili". nayi shiru ban ce komai ba. ita ɗin ma shiru tayi tare da tsura min ido, kallona take cike da zurfin nazarin son gano gaskiyar lamarin. a gefe guda kuma itama damuwa ta bayyana ƙiri ƙiri a fuskarta, tabbas uwa dabance. "zan iya cewa ba ki taɓa min ƙarya ba Sa'ida, fito ki faɗa min gaskiyar abin da yake faruwa kar ki ɓoye min. ba akan kowacce matsala ta gidan aure ake shiru a ɓoye ba, in ta girmama faɗarta ake don a san hanyar da za'a bi a magance, balle ke da kika yi irin wannan furucin kowa yaji ya san lamarin ba ƙarami ba ne". ajiyar zuciya na sauke ina tunanin abin da zance mata, bana so na faɗa mata abunda zai ɗaga hankalinta ya sakata a tsananin damuwa, to amma kuma idan ban faɗa mata ba bayan ita ɗin wa na ke da shi?, idan na ce zanci gaba da ɓoye komai a raina ina barinsa ni kaɗai cutuwa zan ta yi, don haka gwara na faɗa mata ɗin, ita uwa ce, wacca ta shekara kusan arba'in a gidan aure, don haka fahimtar matsalar gidan aure ita ɗin ce kawai, har ta kwantar min da hankali cikin salama. takaicin da ke ƙasan zuciyata shi ya riƙe zubar hawaye na, tiryan tiryan na shiga zayyano mata halin da na ke ciki kusan shekara guda, sai dai haka dole na ɓoye mata zancen dukan da da su Yaya suka min da kuma shi da yace in dawo gida sai ranar da ya neme ni. ta dinƙa kallona da matuƙar mamaki. muryarta a sanyaye ta ce,"yanzu tsawon wannan lokacin kika kasa samuna ki sanar da ni matsalar nan. ai shikenan komai yayi zafi maganinsa Allah, kuma komai yayi farko zai yi ƙarshe, Allah ya magance. hakan kaɗan kenan daga jarabawar gidan aure, sai dai ba kowacce mace ke iya cinyewa ba, a zamanin nan wadda zata yi irin haƙurinki da wuya. kema tun da kika faɗa ba kya jin daɗin zaman tabbas kin gaji da abubuwa ne, to amma ki sani ba ke kaɗai ke cikin irin wannan yanayin ba, mata da yawa basa jin daɗin zaman haƙuri kawai ake ana shanyewa, da za kiji matsalar wasu sai ki ce naki ba komi ba ne, akwai case ɗin auren da naji a radiyo ce nayi idan ni ce sai dai auren ya mutu, to amma ba yanda ka iya, mutuncin mace da darajarta na ga gidan miji, idan ka fito ma zaman zawarcin kansa ƙalubale ne babba. saboda haka ki ƙara haƙuri akan wanda kike yi Allah ba zai barki dawwama a haka ba. daidai da rana ɗaya karki ce za ki ɗauki huɗubar shaiɗan domin zai kai ki ya baroki, a ƙarshe ya barki da faɗawa kogon danasani. kuma ki godewa Allah Sa'ida domin masu matsalar rashin haihuwa da yawa suna gidan iyayensu auren ya mutu saboda ba za'a iya zama da su a haka ba, kuma sun fito an rasa me aurensu. Tabbas mijinki yay ƙoƙari kuma yay haƙuri, in wani ne tuni ya ƙaro aure, kuma matar ta zo da zarar ta haihu ya samu ƙofar wulaƙantaki, don ƙarara zai nuna miki banbancinku. to amma kinga bai auren ba bai kuma da niyya, ba don ba ya so ba sai dan ganin in yay hakan bai kyauta miki ba. babbar matsalarki ƴan uwansa masu shiga hurumin da bana su ba, don haka ki ɗauke ji da ganinki akansu da ita kanta mahaifiyar tasa, in kika nuna musu damuwarki kin ƙara basu gudunmawar cin mutuncin goranta miki ne. ke dai in har kina riƙe da addu'a, nafilfili da karatun ƙur'ani kin gama wallahi, nasara sai dai ta fuskanceki ba dai ta juya miki baya ba, kuma komai sai ya juye miki shi zuwa alkhairi, haihuwa Allahn da ya basu har su ke goranta miki akan ke ba ki samu ba, in sha Allahu kema kafin gushewarsu a duniya Allah zai dube ki ya azurtaki da haihuwar nan su ga ƴaƴanki, amma sam ki daina damuwa da kalmar juya duk da kalmar akwai ciwo, Allah ya saita lamuranki". "Ameen Ummani na gode sosai Allah ƙara lafiya da tsawoncin kwana". ta numfasa kafin ta ƙara cewa,"kuma ina so na ankarar da ke Sa'ida, duk fushin namiji duk wulaƙancinsa akan matarsa ba ya fasa nemanta ya karɓi hakkinsa duk da suna iya jur
🏠