utan gidan tukunna". sai kuma ta Æara cewa,"a'a sai yanzu ma abin yazo kaina, ina Æ´aÆ´an na ki ba ku taho tare ba?".
allon Æirjina naji ya girgiza, na tuna da yaran da nake jinsu yanzu har raina, na ce,"kin san da makaranta, musamman tasu da ba'a fashi, shiyasa na kai su wajen Iyam, amma suna ta rigimar za su biyoni su zo wurinki na ce su bari sai anyi hutu sa zo suyi kwanaki ma".
tana murmushi da ya nuna jin daÉin furucin nawa ta ce,"Allah sarki yaran albarka, wallahi Sa'ida sosai na ji daÉin kyautar nan da aka maki. zan samu lokaci in je har gida in yiwa Iyam Éin godiya".
na yunÆura zan miÆe ta ce,"ke dakata me na ke gani a fuskarki haka? Na ganta a kumbure".
Gabana ya faÉi amma haka na ÆaÆalo guntuwar dariya na ce,"sharrin mura ne...shekaranjiya ta saka min azababben ciwon kai, muka je asibiti suka bani wani magani, shi ne ni kuma saboda tayi saurin tafiya na sha overdose ya juyar min da kai na koma kamar wata Æ´ar maye, garin sakkowa a bene layi ya Éebe ni na Æuma fuska a hannun bene".
ta kalle ni da kyau tana girgiza kai ta ce,"ke kam naga ranar da za kiyi hankali, ina ke ina shan maganin mura har over, ko da ya ke da aka samu Éin ma kika sha".
fuskata ta Æara washewa da gajeriyar dariya na ce,"Ai fa shima haka yayta faÉa".
"ai dole yayi miki faÉa, da kin gangaro daga saman fa?".
na datse maganar da cewa,"Allah ya taÆaita ai, Ummani ni fa yunwa na ke ji mura bata barni na ci komai ba yau, zumuÉin zuwa nan ne ma yasa na kasa tsayawa girki".
"naga alama Éaukin zuwa Æauye yay miki yawa. je ku gaisa Éin kafin ki dawo miyar ta kammala, nima sauri na ke tayi kar uwar tawa ta dawo ta cinye ni Éanya da mitar Kakanta yayi cefane da wuri ni kuma naÆi gama musu abinci".
ta faÉa tana tashi ta shiga madafa. dariya ta ban sosai da ta ce uwarta, Walida ce Æ´ar gidan Yaya Imam, Æ´ar nan ba dai tsufanta ba kamar aljana, tun da aka kawota Yaye shikenan ta zama Æ´ar gidan, tsakaninta da gidansu ziyara, har faÉa ma take ita fa Ummani ce Babarta ba Momi ba, ita da Daddynta Babansu Éaya, duka Abba ne ya haife su.
Gidanmu ba wani babba ba ne sosai, tsaka tsakiya ya ke, sai dai bai saka yawan mutanen da suke rayuwa cikinsa ba sun takura, dan zaka samu kowanne Éangare akwai Éakunan yara har biyu bayan na iyayensu, asalinsa ginin Æasa ne daga baya aka sabunta shi da na bulo a hankali a hankali. gidan gado ne da iyayenmu su ka gada a wajen mahaifiyarsu, don haka ahalin mutum uku ne a gidan da su ka fito ciki Éaya, tun bayan rasuwarta da aka raba musu gado sai suka yanke shawarar zama wuri Éaya don babban burin mahaifiyar tasu kenan, mahaifinsu na raye shi kuma tun da ya samu karayar arziÆi har ta kai ga ya sayar da duk kadarorinsa hatta kuwa da gidansa da suke zaune saboda biyan basukan da ke kansa, shi ne ita Hajiya Umman tasa yaranta su ka gyara nan gidan nata da itama gadarsa tayi suka koma da rayuwa cikin rufin asirin ubangiji, dama ita Éaya ce matarsa har ta mutu, don itama bata rasu ba sai da ta tsufa sosai.
Éangarenmu ne a farkon shigowa gidan, idan ka shiga daga ciki ta tsakiya kuma Éangaren Baba Tijjani da nasa iyalan, shi ne mai mata biyu da tarin Æ´aÆ´a goma sha biyar. sai daga gefen hagu na Éangaren nasa nan Baba Sabi'u ya ke, shima matansa uku amma sun rabu da Éaya, Æ´aÆ´ansa takwas duk mata ne Allah ya ba shi. zaman gidan namu dai kadaran kadahan ne, waÉanda ba su son zaman lafiya Mamu da Æ´aÆ´anta, ita ce fitinanniya a cikin matan iyayen namu, duk wani rikici da zai Éarke a cikin gidan to zaka samu daga gareta ko Æ´aÆ´anta ya soma, kuma da Allah ya tashi sai ya bata kishiya daidai da ita. Mamu da Æ´aÆ´anta akwai baÆin cikin bala'i, ita babban tashin hankalinta taga cikin Æ´aÆ´an gidan wani yafi nata, haka ta tsani taga facalolinta sun fita da wani abun, ko fita za su yi tare taga shigarsubtafi tata to tabbas ta haÆura, Æiri Æiri ta ke nuna hassadarta bata iya Éoyewa, kuma ko da yaushe ita Éin dai ita ce koma baya, shiyasa bama wani girmamata a dalilin abin da takewa iyayenmu da kuma raba tsakaninmu da Æ´aÆ´anta da tayi.
mahaifiyata tana da haÆuri da kawaici, kuma tana cikin irin mutanen da ba su fiya son shiga hulÉar kowa ba, barsu da halinsu su kaÉai sai na jikinsu, bata Æi ka mata abu ba taÆi Éaga kai ta kalleka, Ummani ta Æware a bawa iska a jiyar mutum. amma fa idan aka taÉa mata Æ´aÆ´a to anan ake Æure haÆurinta, anan ake gane bata da kyau ko kaÉan, sam sam bata kawaici ta wannan Éangaren, bata iya bari Æ´aÆ´anta su halaka saboda haÆurinta, haÆurinta ba yasa ta bari a shiga hakkin Æ´aÆ´anta.
dalilin da yasa Mamu ta shafa min lafiya kenan a yaran gidan, ko sharrinta ne ya tashi bata cika haÉawa da ni ba kam, don ta san bakin Ummani ba zai mutu ba akan haka, a cikin ruwan sanyi zata yaÉa mata maganar da zata hanata bacci. Ummansu Hindatu