sa.
"ai wallahi Hajiya ban taÉa taka sa'a a rayuwata ba irin yau, ni dai naji daÉin Éaukarki wallahi. ban san waye ba amma idan rabonsa ce ke Allah ya haÉaku domin ya ce kar in ma yi kuskuren shaida miki shi".
rai na haÉe na ce,"kai Malam ni fa matar aure ce, ko da ka ganni daga gidan mijina na zo gidanmu. kai kawai kaga mutum baka san da ga ina ba ya kama baka kuÉi ka karÉa, to ni da kuÉina don haka ga hakkinka nan, babu ruwana da kuÉin da wani ya baka".
yay Æ´ar dariya da cewa,"ah ban ga kin yi kama da matar aure ba gaskiya, kuÉinki kuma ko na karÉa ma wallahi sadaÆa zan miki da su, gwara ki Éauka ki rage zafi kafin Alhajin Allah ya bayyana a gareki ki huta da hawa abin haya".
ko kusa ko alama tunanin Nazifi a lokacin bai zo cikin kaina ba, idan ma tunanin nasa ya zo ba zan kawo shi ya biya ba dan babu ta yanda za'ai ya Éau wannan uban kuÉin ya bayar kawai kuÉin motar da bai wuce Éari shida ba, abu sai ka ce a film ko littafi, ai ba hauka ake ba, kuÉin ba tsigarsu yake yi ba.
don haka tsaki naja dogo na wuce gida ina faman masifa akan irin Æ´an rainin hankalin adaidaitar nan.
shi kuwa me adaidaita ya murÉa babur Éinsa ya bar Æofar gidan, tafe yake kawai idanunsa na haska masa hoton arniyar motar waccan mutumin, da shi kansa mutumin da kamarsa ta nuna tamkar sarki, ko ba sarki ba to ya ratsu cikin jinin sarauta, irin su ne zaka musu kallo Éaya kasan da ba su taÉa sanin babu ba, haka ba su Æyashin fiddawa su bayar. me Éan sahu dai har ransa yaji mugun tausayin Sa'ida idan har mutumin yazo wajenta taÆi amince masa don yaga da gaske namijin aure ne.
ina shiga gida na tarar da Ummani a tsakar gida tana gyaran alayyawu, ta riÆe haÉa tana kallona ta ce, "Amma dai kuwa Allah ya shirye ki Sa'ida, haka sai da kika taho yanzu?."
yanayin fuskata kuma yasa ta Æara cewa,"to ke da wa kuma daga zuwa sai Éacin rai?".
dafe kai nayi ina zaunawa a kusa da ita na ce,"wani banzan me adaidaita sahu ne mara tunani da lissafi kawai".
ta ce da ni,"ai sai haÆuri, suyi haÆuri da mu muyi da su haka lamarin ya ke. sai ki saki ran naki haka kuma, ni ina zan wani farin ciki ina ganinki rai Éace, ai sai kisa ni a damuwa".
jikinta na faÉa ina kwantar da kaina bisa kafaÉarta ina cewa,"Ummani nayi kewarki sosai wallahi, tun fa mutuwar Inna Talatu ko?". na faÉa ina shigewa jikinta kaman zan koma cikinta.
ta ce,"Kai jama'a, wai Sa'ida kam sai yaushe za ki girma ne ni kam, kita maÆalÆale ni kaman wacce bata bar shan nono ba? To ko dai cikin zan mayar da ke?"
ta faÉa cikin Æ´ar dariya tana mai tarairayo ni jikinta, yayin da farin cikin ganina ke lulluÉe da ita. murmushi nayi ina Æara narkewa a jikinta ina jin wani irin tasirin natsuwa, so, Æauna, salama, jin Æai, na fitowa daga jikinta yana ratsa ilahirin nawa jikin.
na Æara cewa,"Nayi kewar ki ne sosai Ummani, gaskiya mata muna ÆoÆari wallahi, in ba auren ba me zai nesantaka da Éumin jikin mahaifiyarka har akai watanni da yawa".
Ummani ta ce,"to ya za'ai auren kenan, kuma ai ku godewa Allah ma da zamani ya canja, mu lokacin da akayi namu auren tsakaninmu da gida ai sai shekara shekara in dai ba da wani babban dalili ba".
na Éago kai a jikinta ina zaro ido waje in ce,"shekara! tabÉijam, sai ka ce waÉanda aka kai kurkuku, duk haÆurina ba zan iya ba kam sai dai in haÆura da auren".
harara ta watsa min tana dungure min kai ta ce,"ke dai anyi autar gaske, Sa'ida aure sunnah ina ke ina cewa za ki haÆura da shi. hakan ma ki gode Allah mijinki ba mai tsananin kulle ba ne".
"Allah Ummani ko a haka ina jin rashin daÉi, shi ma ai kusan tsananin gare shi akan fita".
"eyy fa to ba laifi kam Nazifi shima ba ya son fita amma ai ba kamar wanda za ki ga sun wuce wata uku biyar babu in da suka leÆa, kuma ke fa duk wata hidima idan ta tashi ya barki kije. kuma ni fa daÉin hakan naji bacin haka Sa'ida in aka biye miki ai rana Éai Éai ne ba zaki zo gidan nan ba".
lafewa na Æara yi a jikinta ina murmushi, ina jin tsantsar farin ciki da jin daÉin kasancewa da ita na ratsa zuciyata. idona a lumshe naji tana cewa,"mage sarkin son jiki sai ki tashi ai kije ki gaida mutanan gidan".
na zame a jikin nata ina cewa,"wai ina su Yasmin da aka barki ke Éaya?". na faÉa ina ÆoÆarin karÉawar wuÆar hannunta ita kuma tana cewa,"waÉannan yaran yanzu ai sai Annabin yabo, kan in Æyalla ido sai dai kiga na neme su na rasa. yanzu fa zancen da na ke miki ban san da fitar su ba kuma da suna zaune nan Walida na kafa min sharaÉan kar in musu miya me yaji".
nayi dariya ina cewa,"sai na fara make Walida in bata yi wasa ba, wato tsabar ta kai Babata ma take kafawa sharaÉi, lallai samun wurin zama, to kuwa rabon in kwasheta in mayar da ita wurin uwatta ne".
Ummani tayi dariya sosai ta ce,"ke da ubanta ai kun fi kusa. ni dai Æyale ni da tayin aikin kije ki gaida m