NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 35 of 97

ta dunƙa zugani akan in juya masa baya in koma baccina amma sai naji ba zan iya ba, haka na miƙe zaune kamar ina so kamar bana so nama kasa gane kaina. shi dai yana tsaye kamar wani gunki kallona kawai yake yi, ya shirya cikin manyan kaya riga da wando na yadi milk colour, yayi bala'in kyau kansa babu hula. kasa daina kallonsa nayi saboda masifar kyawun da yayi min, ba tare da shiryawa ba murmushi ya suɓuce min yayin kallonsa, kalmar kayi kyau na ke shirin faɗa masa, amma sai dai saƙon da ke a saman fuskarsa yasa na sunkuyar da kaina ƙasa na ce,"Ina kwana". Maimakon amsa gaisuwar tawa sai ji nayi ya ce,"Kafin nan da awa guda ki tabbatar kin tattara kayan ki kin bar min gida, kije gidanku ki zauna har sai san da na neme ki". a zabure na waro idanu waje har ban san lokacin da na sauko akan gadon ba saboda ruɗani, hannuna dafe da ƙirji idanunsa cikin nawa na ce,"Hubbi me ka ce?". ransa a haɗe tamkar hadari ya ce,"Kinji ai ba kya buƙatar na maimata miki, ki tabbatar kafin na dawo kin bar gidan nan in ba haka ba za ki yi karo da abin da ba ki taɓa karo da shi ba, wallahi muddin na dawo na sameki sai na miki wulaƙancin da kare ma ba zai shinshina ba". ya faɗa yana nuna ni da yatsa, kafin ya fita ya barni tsaye cikin maɗaukakin mamaki da tsantsar al'ajabi, haka na ƙame kamar gunki ƙofar kawai na ke kallo idona ko ƙiftawa ba yayi, tashin hankali da firgicin da su ke zuciyata kuwa tamkar zata faso ƙirjina ta fito. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un". na faɗa a bayyane ƙirjina yana harbawa hannayena har lokacin dafe da ƙirjina. "lamarin har ya kai haka?, duk haƙurin da na ba shi?, wanne irin bala'i ne wannan?, in tafi gida fa har sai ya neme ni, me yay zafi har zai yanke tsatstsauran hukunci haka? akan dai iya abin da ya faru jiya ko kuma da wani laifin daban a gefe da ban san da shi ba? to ni kuwa in je in ce da su Abbaa me?". a fili nayi maganar ina jan numfashi sama. daɓas na zauna kan gadon na kafe wuri ɗaya da kallo, cikin kaina na rasa tunanin me zan yi, na kuma rasa inda zan ɗora wannan al'amarin me girman gaske. ban san lokacin da hawaye ya shiga zarya a idanuna ba, lallai ina cikin jarabawa, kuma tabbas na yiwa kaina alƙawarin cinyeta, ba zan taɓa bari na faɗi ba in Allah ya yarda. zuciyata ta fara bani umarnin gaggawar tashi in bar gidan karma ya dawo ya same ni yay min abin da zai zama sanadin bugawar zuciyata a yau, a karon farko naji bana son ganin ko da inuwarsa. haka na buɗe wadrobe ina ɗebo kayana, ina zubawa cikin akwatu ina magana tamkar zararriya. "Me zan ce idan na koma gida? Na ce musu mijina ya ce in je gida sai ya neme ni?, bisa laifin me? da wanne ido zan kalle su in musu bayani? Hasbunallahu wani'imal wakil, Hubbi meyasa! Me na maka a rayuwa Hubbi?". ina kuka sosai haka na gama haɗa kayana, na ɗauko hijabina zan saka wayata da ke kan madubi tayi ƙara, na rufe wardrobe ɗin na ƙarasa da sauri na ɗauki wayar don na shaida kiran Ummani daga ringtone ɗin da na saka mata na Uwa Uwa Mama me share min kukana. sai da na saita kaina da danne yanayin da na ke ciki na ce,"Salamu alaikum Ummani, ina yini". Daga can ɓangaren ta ce,"barkan ki dai Sa'ida, an yini lafiya, ya kike ke da mai gidan naki?." na ce,"Lafiya lau Ummani, duk kuna lafiya?". ta amsa,"lafiya lau, amma ya naji muryar taki kamar ba ki da lafiya." na ce,"Ehh wallah Ummani na tashi da ciwon kai ne yau, yanzu na tashi a bacci ma shisa kika ji muryan nawa haka, dama ina cewa zuwa anjima zan kiraki". na faɗi hakan ina dafe kaina yayin da sabbin hawaye masu zafin gaske ke zaryo min. ta ce,"subhanallah to kin dai sha magani ko?". na ce,"ehh na sha, shi ne ma naji daɗi ai". ta ce,"to Allah ya sawwaƙe. daman maganar zuwa ƙauye zan miki na bikin ƴar gidan Kawu Musbahu, gobe ne tafiyar da safe in Allah ya kaimu, ga shi na ji ki babu lafiya sai dai ki haƙura kya je musu daga baya ko". tamkar anyi min bushara da kujerar makka haka naji maganar Ummani, wani farin ciki ya lulluɓe ni har hakan na bayyana akan fuskata, cikin saurin maganar da ban taɓa yi ba na ce,"lahh ai ciwon kaine fa kawai Ummani, kuma na faɗa miki naji daɗi ma". sautin murmushin manyancenta ya bayyana har ya taɓa zuciyata, ta ce"ke dai kawai za kiyi ƙarfin halin naki da kika saba, to Allah dai ya ƙara lafiya. sai ki faɗawa mijin naki, idan ya barki kin fito da sassafe to mu tafi tare, in bai barki ba kuma kya taho ke ɗaya tun da kuna da direba". na ce,"ai kamar ma na sani muka yi maganar da shi ɗazu, da yake shima yana shirin tafiya za su koma dubai, kin san dama nayi miki magana an gama ginin ɗaya plaza ɗin da ya buɗe. sai na ke ce masa to daga biki kuma sai in ɗan yi kwanaki a gida ya ce babu matsala". ta ce,"ah tou faɗuwa ma ta zo daidai da zama, shikenan to sai kin zo ɗin. kya ce masa ina masa Allah kiyaye". da haka muka yi sal
🏠