a gidan auranta. ko babu komai ki gode Allah da ya baki miji me tsananin sonki da Æaunarki gami da tausayinki. ni dai abin da na ke so da ke kar da ki dinÆa barin damuwa a ranki, hakan zai cutar da ke. kamata yayi duk san da kika kasance cikin halin tsanani, to ki Éaura alwala ki fuskanci alÆibla ki gana da ubangijinki, a gaban mahallicinki ya kamata ki zubda tarin hawayenki, ki Æaskantar da kanki a gabansa kina me roÆonsa cikin kirari da tsarkakewa, shi ya san halin da kike ciki kuma shi zai magance miki. kuma hakan zai sa ki samu rangwamen komai, tun haihuwarki mu ke miki addu'a kuma ba zamu daina ba har mu kai ga kushewa, kuma ina miki alÆawarin Æara dagewa akan yi miki adu'a Ƴata. Allah bai hanaki don baya sonki ba, bai bawa wasu don yafi sonsu akanki ba, kema yana sonki kuma zai ba ki mafificin alkhairi cikin yardarsa da amincinsa. Allah yay miki albarka, Allah ya shiga dukkan lamuranki, ya yaye miki dukkan Æunci, ya kawo miki salama da natsuwa. ayi haÆuri a Æara haÆuri a kuma ci gaba da haÆuri kinji Æ´ar albarka, ina faÉa miki hakan ba kuma zan fasa faÉa miki ba ko da yaushe; haÆuri, uzuri, kawar da kai da kuma yafiya, ki kamasu tabbas kin kama makaman nasara da farin ciki, Sa'ida wanda ba ya haÆuri ba ya uzuri ba kuma ya yafiya to shi ne ke samun naÆasun farin ciki, amma me haÆuri da tawakkali da fawwalawa Allah komai wallahi ba ya tawaya, bayan tsanani sai daÉi da izinin Allah".
yay shiru, ni kuma kukana ya Æwace, cikin muryar da ta disashe da majina na ce,"na gode Abbaa nah, na gode sosai, ubangiji Allah Æara muku lafiya, yaja min da ranku, yasa kuyi kyakykyawan Æarshe".
"amin ya Allah Æ´ar albarka. amma ki daina kukan, ki kuma yi min alÆawarin ba za ki Æara ba".
"in sha Allahu Abbaa".
"zan tura miki kuÉi sai dai kiyi hakuri babu yawa".
"na gode Abbaa Allah Æara arziÆi da wadata"
"amin ya Rahman, sai gobe kwayi waya da Ummanin, kar taji ki a wannan yanayin ta hana kanta sukuni, Allah ya sadamu da alkhairinsa, ki gaida Éan nawa".
ya Æarasa faÉa yana kashe wayarsa, wani sabon kuka na Æaunar mahaifina ya zo min sai dai nayi saurin toshe bakina tunawa da alÆawarin ce masa ba zan ci gaba da kukan ba. kai na kifa a gefen gado ina lallashin zuciyata da tuna kalaman mahaifina waÉanda su ka fara kwantar min da hankali, tabbas ina mai godiya ga Allah bisa ni'imar barmin su da yay a raye. wallahi ina son Abbaana, ban san ya zan kasance ba a duk san da aka ce ba ya raye, ni na sani ta kowacce fuska nayi dacen mahaifa, adu'ata Allah yasa suci moriyata kafin mutuwarsu, ya kuma sada su da aljanna maÉaukakiya.
banÉaki na shiga nayi wanka, bayan shiryawata na shiga laluba jakar makarantata, cikon hukuncin ubangiji sai ga shi na samo wata matacciyar Éari biyu, hamdala nayi ga Allah ina miÆewa na fita cikin Éan guntun farin cikina na samun kuÉin, wurin me gadi na isa na ba shi na ce ya taimaka ya siyo min maganin ciwon jiki, idan akwai sauran canji ya siyo min awara ko gurasa. cikin mintunan da ba su haura ashirin da biyar ba sai ga shi ya dawo, nayi masa godiya sosai sannan na koma Éakina, awarar Éari da hamsin ce ba wata mai yawa ba guda uku, na ci na shiga banÉaki na sha ruwa na kuma sha maganin. har aka yi sallar isha'i ina ta jira ko zan ji motsin dawowar Hubbi amma shiru, ni hankalina ma gaba Éaya na kan halin da aka ce yaran suna ciki, idan na Éau waya zan kira shi sai zuciyata ta kwaÉeni akan hakan, daga Æarshe kawai na aje wayar na kwanta bayan nayi sallar isha'i.
wajen Æarfe biyu na dare na farka firgigit, na sauko da sauri na faÉa banÉaki na yo alwala, sallah na tayar ina ta jero nafilfili kuma cikin kowacce sujjada da tahiya kuka na ke ga Ubangijina, ina mai yi masa kirari da tsarkakan sunayensa, ina roÆonsa da ya kawo min sauÆi a halin da na riski kaina, ya wanzar da alkhairansa a gare ni, ya canja min tsanani zuwa sauÆi, baÆin ciki zuwa farin ciki, damuwa zuwa walwala, tashin hankali zuwa kwanciyar hankali da zaman lafiya.
ni dai cikin ikon Allah tun raka'ar farko na fara jin sukuni na ziyartar zuciyata, haka bayan na idar na Éau Æur'ani na fara karatu, karatun da ban daina ba sai da na ji an fara kiran sallar farko, wallahi zuwa wannan lokacin sai naji zuciya tayi wasaisai, naji tamkar ba'a taÉa dasa damuwa da Æunci ba a tare da ni, haka kawai sai na ke jin wani farin ciki da ban san dalilinsa ba yana ziyartata, naji ina mantawa da faruwar komai yana barin jikina yabi iskar Éakin. har sai da aka yi sallar asuba bayan na gama lazimi na ji bacci ya ziyarci idona, a sannan na miÆe da Æwarin jikina da bana jin ciwo ko Éis na hau gado na kwanta, bakina Éauke da tasbihi bacci me daÉin gaske yay awon gaba da ni.
ba ni na farka ba sai Æarfe goma na safe, yau dai hankali kwance na sakko saÉanin da dana ke sakkowa a gigice idan na farka irin haka a makare, ba don komai ba sai don tunawa