NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 31 of 97

, ya ɗauke kansa gefe ya cigaba da abin da yake yi. "Hubbi". na sake maimaitawa ina kallonsa, nan ma shiru. gaban ƙafafunsa na duƙa ina riƙe ƙafarsa alamu na neman yafiya. "Hubbi magana na ke maka fa, na san nayi maka laifi amma kayi haƙuri ka yafe min, kafi kowa sanin halina ba zan hana su Atika abinci haka kawai ba. Meye ribata in na hana su abinci?, wallahi ko wasu ƴaƴan ba zan hana abinci ba balle kuma su da su ke ƴaƴana". magana ya fara, sai dai maganar ya ke yi tamkar ba da ni ba, ni kuma nayi cak saboda kiɗima ina kallon bakinsa da ke motsawa. "shugabar makarantarsu ce ta kira, ta shaida min an kai ɗaya daga cikin yarana asibiti har an kwantar da ita, in yi gaggawar zuwa domin akwai ɓuƙatuwar kashe kuɗaɗe. ina zuwa likitan ta shaida min ciwon ciki ne amma sun ɗauki hoto anyi gwaje gwaje, tun bayan awa biyu yanzu Atika na cikin matsanancin hali na rayuwa, bata farka ba, har yanzu bata motsa ba Sa'ida! bata samun isassan abinci a cikinta haka likitan ya faɗa". yay shiru da maganarsa, naga ya ɗauko ƙaramar takarda alamun daman ita yake nema tun ɗazu, ya tura durowar ya kulle sannan ya gifta ni zai wuce na riƙe hannunsa na ce,"Dan Allah Hubbi kayi haƙuri, wallahi ban san bata da lafiya ba, ban kula ba kuma bata faɗa min ba". Zafin hannunta shi ya ratsa shi sosai hakan ya tabbatar masa da zazzaɓi ne a jikinta bana wasa ba, ya kalli fuskarta yaga duk ta canja ga gefen bakinta a fashe, zai so yay tambaya akan silar ciwon, sai dai ba ya son jin wani ba'asi, hasalima fuskarta haushi take bashi. ganin irin kallona da yake min sai na ɗauka ko ya fara sauka ne, sai na sake marairaicewa ko Allah zai sa ya fahimce ni, kumburarrun idanuna na hawaye na ce,"don girman Allah ka bawa zuciyarka salama ka tsaya ka fahimce ni. Hubbi kana yawan min nasiha akan fushi da haƙuri. Hubbi ka tuna wata rana da nayi fushi da kai tunasarwar da kayi min?...ka faɗa min fushi tamkar taɓin hankali ne ƙarshensa Nadama ne...ka tunasar da ni cewa fushi shi ne tarkon abin da shaiɗan yafi amfani da shi wajen halaka ɗan adam. haka ka ƙara tunasar da ni da faɗin manzan Allah(SAW) akan maganin fushi; yace idan kai fushi idan kana tsaye ne ka zauna, idan kana zaune ne ka kwanta ko kuma kabar wurin da aka saka kai fushin...Hubbi ka tuna...". bige ni yay yana ƙwace hannunsa, ya nuna ni da yatsa yana cewa,"ba ki kai nayi fushi da ke ba...na sani kina so na sakko ne saboda na buɗe miki kitchen, to kinyi a banza wallahi don ba zan buɗe ba sai dai kema a kai ki asibitin, ai yanda kika hana yarana abinci kema haka za ki kwana babu abinci a cikinki, in yaso ki ɗanɗana abin da suka ɗanɗana. Useless woman". ya faɗa yana hararata ya shige ya fita ya bar min ɗakin. nayi murmushi mai ciwo kan abin da ya faɗa, ban da abinsa ta ya zan nemi wani abinci a wannan halin bala'in da na ke ciki?, ta ina abinci zai samu gurbi a cikina?, ai hakan ba abu bane mai yuwa a wajana. ina jin tashin motarsa alamun ya ƙara fita, na jawo ƙafata na fito daga ɗakinsa na koma nawa, na kwanta a kan gado nayi lamo jikina duk ciwo yake min, ina ta karkarwar sanyi. Haka na yini a kwance cikin matsananciya damuwa, ɓangare ɗaya cike da fargabar dawowar su Yaya haka kuma cike da tsananin tsoron hukuncin da Hubbi zai yanke. tashi kawai na ke in shan ruwa in koma in kwanta har magariba babu abin da ya shiga cikina sai ruwa, na galabaita sosai ga ciwo ga yunwa ga aman ruwa, kwata kwata na rasa me ya ke min daɗin a duniyata, ban isa na tuhumi ubangijina kan jarabawa da ƙaddarar da su ke ta ƙwallo da ni ba tun aure, sai dai zan roƙe shi da ya bani ikon cinyewa zuwa matakin nasara. bayan nayi sallar magriba ina zaune jugum, lokacin na kira wayar Hubbi yafi sau goma bai ɗaga ba duk saboda naji ya jikin Atika, hatta ita Yaya da Iyam sai da na kira su amma babu wanda ya ɗaga wayata, ban san wanne asibiti ba ne balle na bi bayansu, sai Lubabatu na kira tace min duk suna asibiti itama an barta ne da yara a gida, amma sun yi waya ance jikin da sauƙi. ajiyar zuciya na sauke don sai a sannn na sami relief, na kwantar da kaina gefen gado ina jan carbi, cikin tunanin da na ke zuciyata ke faɗa min ya kamata in kira mahaifina mu gaisa don mun kwana biyu bamu yi waya ba. duk da ina fargabar in kira shi saboda yacca zai saurin gano damuwar da ke kan muryata, haka na daure na danna kiran saboda ko ba komai waya da shi ɗin zai yaye min damuwar da na ke ciki. nemo lambarsa nayi, nafi ƙarfin minti uku ina saƙa da warwara akan in kira ko in fasa, can kawai na danna kiran ya tafi, kamar yanda ya saba duk lokacin da na kira shi yauma hakan ce ta kasance, ya katse kiran nawa sannan ya biyo baya. da adu'a na samu raunina ya ɓoye da na ɗaga wayar nayi sallama. "Salamu alaikum Abbaa". "Wa'alaiki salam da ma'aikaciyar lafiya, Ƴar albarka ya aka yi saƙon zuciyata ya iso gareki da wuri hak
🏠