NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 29 of 97

iƙe jiki babu ƙwari ina matuƙar jin jiri, a daddafe da bango na fita daga falon zuwa farfajiyar gidan. can ta bayan gidan na nufa wajen da shuke shuken fulawoyi su ke, na nemi manyan duwatsu da busassun itatuwan fulawa da aka ciccire na haɗa murhu, na gangaro durum na kawo shi bakin tagar kicin. takawa nayi na zura hannu ciki, da dabara na samu na buɗe murfin durowar sama da ƙyar tukunna na lalubo ashana, dama tagar da ɗan faɗinta da haka nayi nasarar ciro ƙaramar tukunya. zuwa nayi na iza wuta na ɗora tukunyar, sannan na dawo na gangara durom ɗin zuwa tagar suto, shi dama ana iya shiga ta tagar don haka na shiga ta ciki na ɗebo macaronie da kayan sarrafata wajen girkawa, cikin sauri sauri na ke komai gudun kar mai gidan ya dawo. a wurin me gadi na aro wuƙa da ce masa na nemi tawa na rasa, don haka yankan kayan miyan nayi tun da babu abin jajjage. nan da nan na tashi jalof ɗin macaronie, adu'a na ke tayi ta dahu da wuri har in samu na zuba akaiwa ƴan makaranta abinci tun da break biyu su ke fitowa dama, babu ƙaramin cooler da zan zuba musu abincin don haka ɗakina na koma dole na lalubo wani ƙaton flask me guda ɗaya, ashe da ranarsa da har ina cewa Kakarmu da ta bani bana so, a cikinsa na juye musu abincin na rage kaɗan wanda zan ci. bayan na kammala haɗa musu komai ina sauri in fito in kaiwa Me gadi ya taimaka ya kai musu, isata bakin kofa in ɗaga labule na jiyo kamar tashin hayaniya daga compound, sai dai kafin nayi wani tunani akai aka cakumar min wuya. tsoro yasa na ambaci sunan ilahu da ƙarfi, sai dai idona na sauka kan wacce ke damƙe da wuyana abin ya bani girgiza ni. Anty Aysha ce sai huci take tana hararata, gaban rigata na ƙara kallo in da ta cukume da kyau, kafin nayi magana Anty Aysha ta riga ni da cewa, "don bura'ubanki wacece ke?, wanne kalar jahilci ne cikin kanki?, uban me kike gadara da shi a cikin gidan nan da kike ganin kin isa ki yi kowanne kalar iskanci ki zauna lafiya?, to koma me kike ji da shi yau zan banbance miki tsakanin aya da tsakuwa, zan sauke miki kowanne kalar buyagi Sa'ida, tabbas yau za ki ciji yatsa kina me nadamar abin da kika aikata don kutumar ubanki". baki sake na ke kallonta da maɗaukakin mamaki, ba kalaman ba ne su ka shige ni, zagin shi ya girgiza ni. ko ban kasance matar ƙaninta ba ina ganin ai babu dacewa ta danƙara min zagi na rashin ɗa'a irin haka. sai dai kafin na kai ga wani motsi Yaya da ta iso ta ɗauke ni da gigitaccen marin da ya kai ni kifewa ƙasa, sai dai nayi jarumtar riƙe kaina a tsaye. kuma kafin zafin marin ya sakeni ta ƙara min wani ta ɗaya ɓarin, wanda a ruɗe na ɗago ina ƙoƙarin ƙwace riƙon da Anty Aysha tayi min inyi ta kaina. ganin hakan Yaya tace,"Au ƙoƙarin ƙwacewa ma kike?, guduwa za ki?, To bara nayi miki dukan tsiya sai naga da wanne ƙarfin za ki ƙwace ki gudu, Sa'ida ai yanda kika kwantar min da Yarinya a asibiti kema sai na illataki wallahi". tana faɗin hakan ta fara dukana, duk inda hannunta ya kai a jikina nan take duka kamar wacce ta samu ganga, ni kuma duk wannan bala'in da na ke ciki tunanina ba ya ga in ƙwaci kaina ko in ɗau matakin cin zarafin, a'a hankalina da tunanina na kan furucinta na cewa na kwantar mata da ƴa a asibiti, wacce ƴar?, mene dalilin kwanciyar?, kar dai sharri yaran su ka haɗa min?, waɗannan su ne tarin tambayoyin da ke cikin kaina kuma amsarsu kawai na ke da buƙata. sai da na farga daga hallakanin da suke shirin yi tukunna na fara kiciniyar ƙwatar kaina, amma ina sun riƙe ni gam sai dukana su ke babu ta yanda za'ai na iya ƙwacewa kun san ance sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi. "Yaya ki daki cikin shegiya tunda babu uwar komai a ciki sai kashi". Anty Aysha ta faɗa tana kallon Yaya. Ai kuwa kamar Yaya na jiran tuni akan hakan ta dunƙule hannu ta daki cikina da ƙarfi. "Wayyo Allah!". na faɗa da ƙarfi jin azaba wacce ban taɓa jin irinta ba a cikina. cikani Anty Aysha tayi ta duƙa ta ɗaga ƙafata nayi baya na kifa ƙasa, ta saka ƙafa ta dakar min kwankwaso, a wahalace na runtse ido ina kuka amma hakan baisa sun daina dukana ba. da dukkan iyawata na tattaro ɗan ƙarfina na ture su daga jikina, naja baya da sauri ina ɓoye kaina. idonuna masu zubar da zazzafan hawaye ya tsaya cak akan Yaya wacce ke numfashin wahala tana girgiza, yanda take abin ba zaka taɓa sanyata cikin sahun manya mutane ba, ba ƙaramar mace ba ce, sai ƙwaƙwalwarta kawai da ke aiki da ƙarancin shekaru, zancen da na ke muku tana kan shekaru arba'in da ƴan kai ne. "bagidajiya ƴar gidan ƙananun mutane, shashasha wacce bata ajiye komai ba. ke har kina da ikon hana ƴarmu abinci a cikin gidan ƙaninmu?, wawiya kawai, ba ki san da cewa ta fiki dajara da ƙima a idanun mai gidan ba?, ko mancewa ki kai da ana rabuwa da uwa a zauna da Ƴaƴa?...ko kuma ganin an zuba miki ido kina zaune ke
🏠