kansu, idan na ce zan fanÉare ba su isa ma su min kallon banza ba, to bana son tashin hankalin iyayena da damuwarsu, sannan kuma ina tsoron abin da zai jawa igiyar aurena samun matsala.
duk matsaltsalun da ke ta faruwa da sanin surukata, tun ina zuba ido in ga ta tsawatar akan abubuwan da Æ´aÆ´anta su ke min naji shiru, ga mamakina ma sai na ga tana goyon bayansu, itama ta hau kan layinsu, Æ´aÆ´anta su min, Éanta yay min, itama tayi min. gaba Éaya na rasa ta ina Æiyayyar ta samo asali, na rasa laifina. idan na bada haÆuri sai ya Æara zama wani babban laifin, abin da na lura da shi ma ba akan rashin haihuwa kaÉai yasa su ka tsane ni su ke tsangwamata ba, akwai wani dalili na su a gefe wanda su ka barwa kansu sani.
tabbas babu babban tashin hankali a gidan aure irin ace uwar miji ta sanyo ka gaba, ni a baya ban san wani matsalar uwar miji ba, idan naji Æawayena suna Æorafi akan uwar miji sai in ce ku ne dai baku iya zama da ita ba, ku sota tamkar mahaifiyarku sannan ku mata biyayya kamar taku mahaifiyar, to duk sanda na faÉi haka Hassana Tijjani ta kanyi murmushi kawai ta ce Sa'ida ba za ki gane ba, in uwar miji na sonki tana sonki kawai, in kuwa bata sonki to wallahi duk son da Éanta ke miki zaman auren ba zai taÉa yi miki daÉi ba, in kuwa tana sonki to ko Éanta bai sonki kya sami Æ´ar salama, ita uwar miji idan ta sako ki gaba duk wani kalar biyayya da za kiyi mata a banza ne, ashe hakan da su ke faÉa gaskiya ne domin kuwa ga shi ina ga ni, kallon banzanta gareni ya fi tsorata ni fiye da na Éanta.
duk wannan tashin hankalin da na ke ciki iyayena da Æ´an uwana babu wanda ya sani, ban taÉa faÉa ba kuma ban taÉa nunawa ba, sai dai kawai fa duk wanda yay min farin sani yana ganina zai ce ina cin matsala, hankalina ba'a kwance yake ba. domin kuwa lokaci guda na fita a hayyacina na Æara yin wata muguwar rama, nayi duhu duk na sakwarkwace, na zama kamar mara lafiya ÆwaÆwalwa saboda kullum a firgice na ke, haka na ke jin duk rayuwar ta fita a raina, har so na ke dare yayi Éarawon bacci ya Éauke ni in sami Æ´ar salama, don bani da babban tashin hankali sama da wayewar gari, da zarar gari ya waye na shiga fargaba da taraddadi kenan.
uhmm so kenan, wallahi duk wannan tsananin da na ke ciki na gidan aurena har yanzu banji soyayyar mijina ta taÉu a raina ba, ban ji ina nadamar aurensa ba, ban taÉa jin ina ma ya sawwaÆe min in huta ba, sonsa na ke da dukkan raina, sam bana fushi da duk abin da yake min, uzuri na ke masa da kuma adu'a, tun bayan aurena da shi ban canja akalar adu'ata ba, kafin na yiwa kaina shi na ke yiwa, ni har na fi so ya zo yana min bambami akan ya shareni kwata kwata babu magana, kuma kullu yaumin bana fasa zuwa neman yafiyarsa da basa haÆuri a kowanne daren rana kafin kwanciyata, zan ta haÆuri ba zan karaya ba, Allah na zan ta faÉawa ya daidaita tsakaninmu, ya kuma bani ikon cinye jarabawar.
yau na tashi da matsanancin ciwon kai, hakan yasa na kasa fitowa gaba Éaya, tun da nayi sallar asuba na durÆufa kan sallaya, bacci ma na ke so na koma amma na kasa saboda gabana da ke ta faÉuwa, ga shi ina so na tashi in je in tada yara su yi shirin makaranta sai dai in na tashi jiri sai ya mayar da ni.
da Æyar dai na lallaÉa na tashi a daddafe na fita, Éakinsu na shiga, na shiga banÉaki na tara musu ruwan wanka, sannan na fito na tashe su kan suyi wanka. su ka tashi da Æyar kowacce na faman Éata rai, zama nayi ina lallashinsu da ba su haÆuri akan cewa watarana sai labari, yanzu ne su ke da dama da lokaci na yin karatu, idan basu yi ba nan gaba za su ciji yatsa.
na lallama su da Æyar su ka sauko su ka wuce banÉakin, na jaddada musu da su yi sallah in sun shirya. Éaki na koma saboda sanyin zazzaÉi da ya rufe ni, ina shiga na Æudundune cikin bargo ina ta karkarwa, kaina jinsa na ke kamar zai faÉo, haka cikina ma wani bala'in ciwo ya ke min. ban ankara ba kawai naji amai, duk ÆoÆarina na kar in yi akan gadon hakan sai da ya faskara, amai nayi sosai mai wahalarwar gaske. gaba Éaya jikina sai ya saki, da Æyar na kimtsa wajen a wahalce na dawo na kwanta, hawaye kawai na ke zubarwa saboda ni Éaya na san irin azabar ciwon da na ke ji a jikina.
ina cikin wannan halin aka turo Æofar Éakin, Rumana naji tana cewa,"Anty mun gama shiryawa".
fito da fuskata nayi ta cikin bargon kaÉan, bana iya ko ganinsu da kyau, murya a wahalce na ce da su.
"wayata na kan mudubi Æarfe nawa?".
Atika ta duba tana cewa,"seven twenty".
idona na rufe, har ga Allah ban da wani Æarfi da Æwarin da zan tashi in dafa musu abinci. a hankali na ce da su,"Rumana ban da lafiya, ku yi haÆuri kuje kitchen akwai sauran abincin dare a flask Éin Abbanku ku ci kun ji, na san bai huce ba. abincin makaranta kuma zan bayar a kawo muku".
su ka yi shiru ba su ce da ni komai ba duk su ka yi cirko cirko. tsoron abin da zai biyo baya yasa na miÆe za