NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 24 of 97

cikina ina rufe idanuwana tare da roƙon Allah ya azurtamu da haihuwa kafin mutuwa. farin cikinsa ya kasa ɓoyuwa, abin da ya siyo musu ya basu suma sai murna su ke yi, wayarsa ya ɗauko ya kira Yaya yana ƙara yi mata godiya da alkhairinta gare shi, Anty Aisha ma ya kirata daga baya. ya tambayi yaren sun ci abinci suka ce masa ehh, yace to su taso suje ɗakinsa, a tare muka fita gaba ɗaya muka bi shi, haka naci albarkacin yaran walwalarsa gareni ta dawo, mu ka ta hira kamar ba shi ba da ya canja ƴan kwanaki, bini bini ya tambayeni me ya kamata a siyawa yaran, ni dai abin da na fara cewa shi ne akai su makaranta da wuri gudun kar ayi musu nisa a karatunsu. bayan ƴan kwanaki da safe na fito a wanka, turus nayi ganin Hubbi ya shigo ɗakin wanda rabonsa da ɗakina har na manta. kallonsa na tsaya yi wanda shima ya ke bina da kallo, to da yake dai tun zuwan su Atika ya ɗan sakko tsoronsa ya ragu a raina, muryata a hankali na ce,"ina kwana". ciki ya ƙaraso yana zama bakin gado. "kin tashi lafiya". "lafiya lau, mun je ɗakin ai na tarar baka tashi ba. na ɗauki ɗari biyu a wallet na bawa su Rumana kuɗin makaranta". na ƙarasa gaban madubi na ɗauko takarda ƙarama na miƙa masa ina daɗa cewa,"jiya aka basu a makaranta wai sun manta ba su baka ba". ya kalli takarda yana cewa,"ta mece?". "ban duba ba". karɓa yay ya duba ya ajiyeta. sai kuma ya kishingiɗa da gadon yana danna wayarsa. ni dai tun fitowata daga wankan na ke jin tasirin kallonsa na shiga jikina. tun da aka bamu yaran nan naga ya dawo hayyacinsa, kuma alamunsa sun nuna ya gaji da ƙauracewa junanmu, so ya ke ya kasance da ni sai dai ni ɗin kuma na ƙi basa dama da fuska, don ko jiya da naga take takensa na agwiwa ya ke ɗaki na gudo. yi nayi tamkar na mance da shi a ɗakin, na buɗe wadrobe na ɗebo kayan da zan saka, sannan na ƙarasa na zauna kan kujerar madubi, ta cikin madubi na hasko shi idanuwansa sun kafe a kaina. cikin natsuwa na yin komai nawa a hankali na ɗauko man shafawa ina shafawa, tun da na shafa humra na hasko ya lumshe ido yana sauke ajiyar zuciya. na ƙarasa kimtsa jikina da turaruka cikin salo na jan hankali, ina gamawa na wuce zan saka kayana sai naji muryarsa a kasalance yana cewa. "zo". ɗago ido nayi na kallesa naga yanayinsa duk ya sauya. rigar nayi ƙoƙarin sakawa ya sake dakatar da ni da cewa,"ki zo na ce fa". ina ɓata fuska na ce,"Hubbi bari na ƙarasa saka rigar...". sai da na saka sannan na je wurin nasa, ya ɗago fuskata yana kallona ya ce,"Habibty fushi kike da ni?". kai tsaye na ɗaga masa kai, sai kuma hawaye ya sakko min. kwanto kaina yay saman kafaɗarsa da cewa,"ba kya kewata?". cikin muryar kuka na ce,"idan ma nayi kewar taka ya zanyi Hubbi, ka mayarshe ni tamkar ba matarka ta so ba, ka ƙi faɗa min dalilinka na ƙaurace min, duk na baka haƙuri ka ƙi haƙura, ban san laifin da nayi ba ka daina sona". ya zago da hannayensa ta ƙuguna ya ce,"to kiyi haƙuri na san na miki ba daidai ba, afuwan kin ji". yay maganar ƙasa ƙasa da muryar lallashi. na ƙara cewa,"to me yasa hakan Hubbi?". numfashi ya sauke ya ce,"saboda ina so inga na sami ɗa sai dai ke kuma shiru, naga kamar rashin haihuwar bai damunki, shiyasa na ke ganin mu'amalar tamu ma bata da wani amfani. amma yanzu da na sami yarancan sai na ji kaso saba'in ya yaye na damuwar rashin haihuwar da bamu yi ba. amma kin sani ina sonki, matsayinki bai taɓa canjawa ba daga gare ni, don haka kar ki ƙara cewa na daina sonki kinji ko, ni na ki ne na har abada, ke ɗaya jallin jal Sa'idan Nazifi". murmushi nayi ina kallonsa, jin maganganun nasa nayi kamar daɗin baki, sai dai kuma ba hakan ba ne, tabbas shi ɗin mai tsananin sona ne duniya kanta zata shaida hakan. sabuwar soyayyarsa naji ta kamani, sai dai na kasa amayar da duk wata magana da ke narke a cikina. duk tarin baƙin cikin da ya ƙunsa min naji ya gushe, tabbas ina son Hubbi, ina ƙaunarsa, kuma sonsa da ƙaunarsa ne yasa zan ci gaba da haƙurin rayuwa tare da shi ɗin, domin a ƴan kwanakin nan kaɗai na lura soyayya da komai nasa da ya tattare ya ɗora akan yaran can zai iya haifar min da babban ƙalubale. "ya kamata mu sha soyayyar da zata mantar da mu komai da ya faru, komai ɗin ya zama tarihi". ya katse tunanina da faɗin hakan. kuma lokaci ɗaya naji yana tattare rigata zai cire. lokaci guda ya fara aika salonsa ga jikina, tuni kuma na biye masa muka faɗa cikin duniyar jin daɗin ma'aurata, mun daɗe kafin mu sami natsuwar da muka rasa na tsawon watanni. da mamakina muna gamawa ya tashi ya fita a ɗakin ko wanka bai tsaya yayi ba, saɓanin da anan yake wankansa, wataran ma tare mu ke yi, mamakin hakan ya tsaya min a rai. na miƙe cikin gajiyar jiki na shiga wanka, ko bayan fitowata kasa komai nayi sai kwanciya saboda ba ƙaramin gajiyar da ni yay ba, sai da ya ƙosar da kans
🏠