daÉi, har sai kunnenki yay rawa".
su ka Éanyi dariya Rumana na cewa,"ferfesun kaji?".
kai na gyaÉa na ce,"ehh har da shi, sai kuma dashishi".
Rumana na tsalle ta ce,"irin wanda Ummaa ke yi?".
na Éaga mata kai tabbacin haka. duk Éin su suka kama murna, ina riÆe da hannayensu muka wuce kitchen. a tray na zuba musu na sanyo musu ferfesun naman kazar a bowl, su ka taya ni Éauko wasu muka fito, nan kan carpet na ajiye musu su ka zauna su ka fara ci ni kuma na juya kitchen Éin don zubowa su Yaya na su.
kiran Hubbi ya shigo wayata na Éaga ya ke shaida min ga masu furnitures Éin nan sun zo. na fita na hau saman na shaidawa su Yaya, sai sannan na ke Æara ganin ashe ma basu kaÉai ba ne har da nasu baÆin wanda su ka zo da su suyi musu gyaran. cikin su biyun dai babu wacca ta tanka min bayan waÉancan da su ka gaishe ni. na juyo na sakko ina faÉawa me gadi yaywa ma'aikatan iso, ai na fita hakkinsu tun da na sanar musu za'a shigo.
ina Éakin Hubbi na jiyo muryar Yaya na kwakwazon faÉa,"mene haka na ke ganinku zaune a Æasa kamar wasu almajirai, don me Nazifin ya siyo wancan dining Éin ya ajiye, ko dama na kwalliya ne?, kai ku tashi ku koma can ku ci abinciku, kar a Æara baku abinci ace ku zauna kan kafet ku ci. ba baÆi ba ne ku, nan gidanku ne gidan Babanku, kuyi yanda kuke so yanda ku ka ga dama kar ku ji shakkar yin komai, duk abin da ku ke so kuyi magana da Babanku, idan Antyn tayi muku wani mugun abun ku dinga faÉa masa kun ji ko".
sai kuma Anty Aisha ta Éora da faÉin,"umm ni dai Yaya ban da kin ce wallahi yaran nan ba za su zauna ba. ji fa don Allah yanda aka barsu su kaÉai a falo kamar wasu marayu, wallahi ko baÆo aka yi sai ya ce Æ´aÆ´an ruÆo ne bana gida ba, don an bambamta Æiri Æiri. to ni dai har ga Allah ina ganin wani canji da ban gamsu da shi ba zan zo in Éauke yarinyata, ba zan cutar da kaina ba akan yiwa Æanina kara".
da babbar murya Yaya ta Æwala min kira, kamar wacca aka hankaÉo daga Éakin sai ga ni na fito jiki sai Éari ya ke yi. a dabarbarce na ce,"kun sauko, ga abincin...".
"ke dilla can dakata banza mara mutunci, ba yunwatattu ba ne mu, da fari ma in tambaye ki, nan gidan waye?".
kaina a Æasa murya na sarÆewa na ce,"gidan aurena".
tayi wani makirin murmushi da sake cewa,"to gyara zancenki, domin ko yanzu ba sai anjima ba kina iya barin gidan nan ki tafi a fanko, nan gidan Nazifi ne, Nazifi kuma Æanina ne, ba Æ´an uba mu ka haÉa ba uwa Éaya uba Éaya tafi gaban wasa, duk abin da yake mallakina yana da iko da shi kamar yanda duk mallakinsa ina da iko da shi. soyayyar da mu ke yi masa da tausayinsa yasa mu ka Éauki Æ´aÆ´anmu mu ka ba shi, wannan yaran da kike gani ba bare ba ne yanzu, ba ki da ikon kallonsu ki ce nan ba gidan ubansu ba ne balle kiyi musu iyaka da shi, yanzu Nazifi ne uwarsu ubansu, su kuma ko yau Nazifi ya faÉi ya mutu sun zama magadansa. saboda haka kinga kuwa sun fi Æarfin ki ci mutuncinsu, ba marayu ba ne ba Æ´aÆ´an kishiya ba ne ba kuma Æ´aÆ´an tsintuwa ba ne. ko da kika ganki matar gida ba wai ke aka bawa su ba, mai gidan aka bawa, don haka ki tsaya iyaka matsayinki".
ni dai take takensu da na lura yasa naja baki ban ce kanzil ba, don haÆurin ma idan na bayar zai iya zama wata rigimar, Æarshe ma Æanin na su ya dawo su haÉa masa Æarya da gaskiya, shima ya juye min nasa rashin mutuncin. yaran su ka tashi daga inda su ke suka bi bayan budurwar da Yaya tasa ta kwashe abincin nasu ta kai musu kan dining, can su ka ci gaba da cin abincinsu. yayin da su kuma su ka koma saman don Æarasa gyara Éakin yaran.
ni dai tun da nayi komawata Éaki ban Æara fitowa ba, ina jin duk wani kai komo na su da su ke yi, ba wasu yawa gare su ba amma yanda ka san masu jeran kayan amarya duk sun cika gidan da hayaniya. qur'ani na Éauka ina karantawa don shi zai mantar da ni babinsu, sai bayan sallar la'asar na daina jin motsi, a sannan ne na fito na lura da sun tafi, tafiyar da ko arziÆin sallama ban samu ba.
Éakin yaran na buÉe na leÆa, zaune na gansu kan gado Éaya suna kallo. Atika tayi murmushi da ganin nawa ita kuwa Éayar ta haÉe rai tana juyar da fuska gefe.
na Æarasa wajen na su, Éakin na su yay kyau, gadon yara ne guda biyu aka saka kowacce da nata, sai drowern kayansu ma kowacce da nata, Éakin ya burgeni sosai kam dan dama in ta Éangaren gyaran gayu ne Anty Aisha ba daga nan ba, zama nayi cikinsu ina masu hira wanda har sai da Rumana ta saki ranta, dama ita ce me bakin magana, nan kuma aka shiga bani labarin Æawayen makaranta da malamarsu me sa kamun kunne, har tana faÉa min tun da sun dawo nan ga makarantar da zan ce Yaya Æarami ya saka su.
a haka Hubbinya dawo ya same mu, annurin fuskarsa kaÉai ya shaida min yana cike da tsananin farin ciki, sai naji tausayinsa duk ya kama ni, ya kenan yau in ace Éansa ne na cikinsa?, hannu na kai saman