NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 22 of 97

ri ta Hindatu". wata wawiyar ajiyar zuciya na sauke ina hamdala ga ubangiji, yayin da Hubbi su ka shiga gaisawa da ita yana shaida mata rikicwar da nayi akan rashin ɗaga kiran nata, bayan sun gama ƴar hirarsu ya miƙo min yana murmushin leɓe tare da tsokanata, wanda hakan ni kuma yasa raina sanyi, domin rabona da ganin annuri a fuskarsa har na manta balle kuma murmushi irin haka. cikin wani irin jin daɗi mara misaltuwa mu ke waya da mahaifiyata, kira kawai tayi taji ya muke, ashe ma ko da ta bar min miscalls da yawa ba ita tayi kiran ba Yahanasu ta bawa, ita kuma dama bata iya kiran hankali ba, kusan kullum sai Abba yay mata faɗa akan hakan. muna wayar naji duk damuwata ta gushe, tana ta bani labarai masu daɗi, ni kuma ba ni da wani labari da zan bata wanda zai sanyata farin ciki, sai da naji muryarta ta fara sauyawa wadda ke shaida min tana ƙoƙarin gano cewar ina cikin matsala ne, sai nayi saurin gusar da tunanin hakan a ranta nima na bata labarin su Atika da aka bani, ina shaida mata cewar ma yau za a kawo su, aiko farin ciki kamar tayi me, taji min daɗi sosai tana ta yiwa su Yaya godiya da shi albarka, ta ce ma na bawa Hubbi shima tayi masa murna, ni kuma tayi min nasiha sosai a game da ruƙon yaran. sai kuma kawai naji ta koma ambaton wannan kyauta ce daga Allah na sameta ya bani ta silar wasu, na riƙe ƴaƴana da amana kar in cutar da su, yarda da aminta cewar zan kula da su yasa har iyayen yaran suka bamu duk da cewar sun yi domin ɗan uwansu ne, amma duk da haka don suna da yaƙinin matarsa mutuniyar arziƙi ce yasa su ka ba shi. nasihohinta su ka karayar min da zuciya sosai tun ma inji tana ambaton ƴaƴanki, sai na dinga jin wani irin yanayi na tsarga min a dukka jikina, haka zuciyata ta dinga motsawa, ban san ma ta yanda zan kwatanta abin da na ke ji ba a tare da ni. hawaye naji na sakko min, nasiharta ta ƙarshe abin da tace min,"ki so su tamkar ke kika yi naƙudarsu, kar ki cutar da su, kar ki dinƙa musu kallon ba ke kika haife su ba, ki kuma yi haƙuri da duk halinsu domin ko ɗan da ka haifa sai kayi haƙuri da shi, Allah ya tayaki ruƙo ya albarkaci zuri'a, idan kina da rabo kema Allah ya kawo lokacin muna raye". da haka muka yi sallama da ita, kuka sosai na saki, sama sama Hubbi ke lallashina da ike ma yaji duk wayar tamu. haka na miƙe ina jina wani iri na shiga aikin tarbar ƴaƴana, har na hau sama zan fara gyara musu ɗakinsu sai kuma na ga dai gwara in fara ɗora abincin. na sakko na shiga kitchen. ba ni na gama girki ba sai azahar duk da cewa da wuri na ɗora, to amma da yake dashishi ne yafi dambu wahala shiyasa na jima. ina kitchen ɗin ne na ke jiyo kamar tashin hayaniya daga falo, na wanke hannuna na fita cikin sauri. tsaye na tarar da su Anty Aisha. da fara'ata na ke gaisheta, ta amsa min babu yabo babu fallasa. hannu na buɗewa su Rumana ina murmushin jin daɗi, jikina su ka shige ina rungume su tsam. ba tare da sani ba naji saukar hawaye a kumatuna, na janye su a jikina muna gaisawa da su, yaran suma sai murna su ke yi, dama dai in dai yara ne suna son zuwan gidan Yaya Ƙarami. Anty Aisha ta ce,"ce na ke gidan ma ba kowa da mu ke ta sallama ba'a amsa ba, wannan ai sai a shigo ayi sata ba ki san anyi ba". shirunta ya haɗe da sakkowar Yaya daga saman bene, tana watsan wani kallon banza ta ce,"da kina ciki amma kina jin mutane kika kasa fitowa". "wallahi Yaya banji ba, da yake na kunna radiyo ne ina girki. sannunku da zuwa". "yauwa". ta amsa a daƙile kafin ta ƙara cewa,"Baban yaran nan ya ce ɗakinsu na sama, na hau da kayansu kuma naga ba wani ɗaki gyararre". cikin fargaba na ce,"ehh ɗakin kusa da nawa ne na su, aikin da na ke yi ne ma yasa ban samu na gyara musun ba. da ike za'a kawo gadajensu to su ma masu kawowar shiru naga basu zo ba". Anty Aisha ta ce,"gyara ya hau kanmu kenan, to bara muje mu gyara musu...". na yi saurin tarar numfashinta da cewa,"haba Anty Aisha ban isa ba, saboda su wallahi na ce gwara in gama dafa abincin. amma ai nama gama yanzu zan je in gyara musu". ta wuce ni tana faɗin,"a'a gwara dai kiyi abin da kika saba ki dafa kici ki kwanta. ni ai bana iya tafiya in bar su haka ban ga sun sanya haƙarƙarinsu a makwanci ba, ba zan samu sukuni ba sam, ba da sauƙi nayi naƙudar ba, don ma dai Nazifi ne ban da haka ai wallahi da ƴata zan juya. ka yi sadaukarwar abin da ka haifa sukuntum guda kuma tun ba a je ko ina ba an nuna maka kulawa zata yi wuya, ko da ya ke sanin ciwon ɗa sai wanda ya haifa. Yaya ni nayi nan". zuciyata ta matse sosai da zafi, na mayar da ruwan hawayen da ya cika idona, ban iya cewa komai ba, Yaya ta bi bayanta su ka haye saman su ka bar ni nan da yaran. na maida kallona ga yaran da ke tsaye a gabana, na dafa kafaɗunsu ina ƙaƙalo murmushi na ce,"yaran albarka in zuba muku abinci?". Atika ce ta ce,"Matar Yaya Ƙarami me kika dafa?". na kama kumatunta ina cewa,"abu me
🏠