NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 21 of 97

—aga min hannu,"kuma a hakan kike tunanin za ki fita, makarantar fin mijinki muhimmanci tayi ko me?. to dawo babu in da za ki je sai kin yi duk abin da kika saba kafin ki fita, in kuma ba haka ba ki haƙura da zuwan gaba ɗaya kyaje gobe". sai kuma can yay gajeran tsaki ya ce,"ke bama za kije ko ina ba, yau na soke zuwan". cikin sadda kai na ce,"don Allah kayi haƙuri Hubbi, wallahi bana so nayi fashin zuwa, bari nayi sauri na dafa maka, me zan ɗora?". na faɗa ina kallon agogon da ya kaɗa ƙarfe tara har da minti goma, to yanzu ko da ace ma fitar nayi kafin in je makarantar ai tara da rabi ta wuce, kuma a dokan makaranta minti biyar ka ƙara ba zaka shiga aji ba, kuma ba za'a barka ka dawo gida ba sai dai ka zauna a waje har lokacin tashi, don ma matan aure ne mu ba yanda su ka iya wajen duka. haƙura kawai nayi na cire hijabina na ajiye, na je na mayar masa da kuɗin da na ɗauka. "dashishi za ki dafa da rana, akwai tsakin alkamar ko?". "ehh akwai". "to ki dafa da yawa saboda akwai baƙi". na amsa masa da,"to". zan fita a ɗakin ya dakatar da ni da cewa,"ki gyara ɗakin kusa da ke na sama, Rumana da Atika za su dawo wajenmu, anjima za'a kawo su ko idan na fita in ɗauko su. na sa a kawo musu gado, ban san lokacin da za su kawo ba idan ina nan shikenan, in bana nan sai ki kula". tamkar an kafe ni haka nayi ƙyam a tsaye da jin furucinsa, Rumana da Atika!, za su dawo gidan nan da zama?. anya kuwa?, Hubbin da ya ce ba zai taɓa riƙe ɗan wani ba saboda mahaifiyarsa ta riƙe bata ji da daɗi ba, don haka shi ma matarsa ba zata riƙi ɗan kowa ba saboda sanin halin ɗan ruƙo da ke da wuyar sha'ani. to amma ta ya akai farat ɗaya haka ya ce yaran za su dawo gidan nan?. ya katse min tunani da cewa,"kika kafe ni da ido, Rumana ce Æ´ar gidan Yaya sai Atika Æ´ar Anty Aisha, cikinsu wa ye baƙon fuska a wajen ki?". a rauna ne na ce,"duk ba baƙuwar fuska, amma Hubbi gaba ɗaya gidan nan za su dawo ko hutu za su zo?". "iyayensu sun bar min su halak malak, kinga kuwa ba hutu zai kawo su ba. zan koma Babansu ke kuma Mamarsu, sai ki shirya tarbar ƳaÆ´an da aka ba ki". ƳaÆ´an da aka ba ki! kalmar ta ƙarshe ta daki ƙirjina. Rumana da Atika, gaba ɗayansu ba su wuce shekaru takwas ba, yaran ba su kunya ga rashin ji shisa jininsu ya zo ɗaya, ko iyayensu kuka su ke da halinsu, shi ne ni kuma yanzu zai ce zai ɗauko min su in riƙe a wannan sanyin halin nawa?, salon wataran su fusatani in sauke musu fushina in ƙara baƙin jini, dama ya lafiyar kura bare an taɓota. na san dole akwai wata a ƙasa, sai dai ina roƙon Allah ya ɗora ni a kansu, ya kuma sauya duk wata baƙar manufa da aka ƙulla akan hakan. murmushi na ƙaƙalo na ce da shi,"ai ko dai muna godiya matuƙa, Allah taya mu ruƙo, naji daɗi sosai, ko ba komai ma rage kewa". na faɗa ina nuna jin daɗin da bai kai har zuci ba, domin cike na ke da fargabar rayuwarmu tare da yaran. bai ce da ni komai ba yay shiru, na sauke ajiyar zuciya na fita daga ɗakin. ɗakina na koma na canja kaya, dama a falo na bar jakata da wayata, kuma da zuwan nawa na tarar da kiran Ummani, sai naji gabana ya faɗi ganin miscalls har guda biyar, take na fara tunanin anya lafiya don bata taɓa min miscalls irin haka ba, Ummani duk in da ta kira waya sau biyu ba'a ɗaga ba haƙura take yi, sai tace bata san uzurin mutum ba, idan ya gani zai biyo baya. zama na yi kan kujera jiki na rawa na bi bayan kiran, sai dai ko da kiran ya tafi a lokacin kamfani ke shaida min bani da kati. ƙaramin tsaki nayi na ƙorafi tuna fa ashe tun shekeranjiya muna waya da matar Yashaik katin ya ƙare. ina zaunen Hubbi ya fito, ina kallonsa ɓacin ran hana ni zuwa makaranta ya ƙaru, na kawar kawai na kasa share shi saboda ina so ya bani aron wayarsa. cikin shakkar masa magana na ce,"Hubbi don Allah aron wayarka in kira Ummani". yana zama kan kujera ya ce min,"me ya sami taki?". "babu kati". har zai miƙo min wayar tasa sai kuma ya fasa ya ce,"bari in saka miki katin, wanne layin?". "Airtel ɗin". cikin wasu Æ´an sakanni sai ga saƙon katin ɗari biyar ya shigo, nayi masa godiya sosai. na danna lambar Ummani na kira sai dai haka ta gama ringinga har sau biyu ba'a ɗaga ba. take gabana ya tsananta faɗuwa, ban san lokacin da nayi mazauni a gefen Hubbi ba ina damƙar gefen rigarsa. "lafiya?". a ruɗe kamar zanyi kuka na ce masa,"bata ɗaga wayar ba ne, kuma kaga miscall ɗinta biyar na tarar". ganin yacca jikina ya ɗauki ɓari ya karɓi wayar daga hannuna, yana ƙoƙarin ƙara kiran sai ga kiran Hindatu na shigowa. ya ɗaga ya miƙo min amma sai na kasa karɓa don ban san me kunnuwana za su jiye min ba. shi ya amsa kiran sai dai maimakon muryar Hindatu naji muryar Ummani na cewa,"Sa'ida ina hanya ne shiyasa ban ɗaga ba, kuma na shigo gidan babu kati a wayar sai na a
🏠