mako na ke yi duk da su lafiya Æalau su ke suna haihuwa abin su...ko Malam dai kina ganin yacca yake rubuce su da ayoyin qur'ani, ya kamata gaskiya dai a duba miki rashin haihuwa ai bala'i ne, ga shi ni Allah ya sani ina ta so inga Æ´aÆ´an Nazifi wallahi, Allah yaji ya gani bana so na mutu banga jikokina daga gare shi ba".
nasa hannu na goge hawayen da ya sakko min ba tare da na bari ta lura ba. ban iya cewa komai ba, haka ta rakomu har waje tana ta Æ´an maganganu. kan hanyarmu ta komawa gida babu yacca banyi ba ya faÉa min sakamakon gwajin da aka yi min amma kamar ba muminin da na ke ta haÉawa da ubangijinsa ba, Æememe ma yaÆi min magana.
Muna zuwa gida kowa ya wuce Éakinsa, ni dai ko da na shiga kan gado kawai na faÉa ko hijabin ma na kasa cirewa, kukan zuci na ke yi domin kuwa ruwan hawaye yaÆi sakko min. Ina cikin duniyar tunani wayata tayi ringing, na Éaga ganin shi ne yake kirana. a taÆaice ya ce da ni,"ki zo ina nemanki".
Da damuwa fal a muryana na ce,"me zan maka Hubbi?".
"Me za ki min! Kina tambayan mijinki haka!, lafiyarki?".
Shiru nayi na Æi cemasa komai. kiran wayar sai tafiya yake yi, can yay nisa ya ce,"ai kin ji abin da na ce ko?, to ki taso yanzu kar ki ragen lokacin bacci, in kin zo kya ga me za ki min".
da faÉar hakan ya kashe wayarsa, tashi nayi na shiga banÉaki na wanko fuskata, ban cire kayan jikina ba haka na fita don karma na sanya kayan bacci ya tsammaci ko ina jiran kaÉan ne.
Ina shiga na iske har yay kwanciyarsa ma, na zauna gefen gadon ina kallonsa ta cikin Éan hasken duhun Éakin, a hankali nace masa,"gani, ko kayi bacci?".
zaune ya miÆe ya fuskance ni sosai, ya sauke numfashi sannan ya kira sunana. sai da na Éora idona a saman fuskarsa tukunna na amsa saboda yacca naji yanayin sautin muryar tamkar ba nasa ba.
"Ina da bukatar haihuwa Sa'ida, so na ke na ganni Éa".
nayi wani guntun murmushi mai ciwo, hannuna bisa kafaÉarsa, cikin tausashshiyar murya na kwantarwa da mutum hankali da sanya natsuwa na ce,"to Hubbi mu ci gaba da faÉawa Allah, shi zai bamu ba wani ba, haihuwa a wurinsa kaÉai take ba ga wani mutum ba, damuwarmu ba ita zata sa mu samu ba, Æosawarmu ba zata bamu ba, haÆuri da jiran lokaci Hubbi".
"kina nufin ke ba za ki iya haihuwar ba kenan?...".
Na katse cewarsa da,"Subhanallah, baka ji abin da nace ba ne kake ambaton ni ba zan iya bawa kaina ba. Haba Hubbi kar son wani abu yasa ka yi saÉo, ai ba zancen ba zan iya ba, idan Allah ya kawo mai zai hana kuwa in haifa maka Æ´aÆ´a, in bai kawo ba ina da ikon bawa kaina ne?, haÆurin nan dai da muka saba shi zamu ci gaba da yi, komai lokaci ne, watarana sai Æalubalen jinkirin kaga ya zama alkhairi mafi girma".
aikuwa furucin nawa ya fusata shi, nan ya hau banbami yana faÉin,"fina sanin daidai kika yi da za ki dinga tsara min kalamai, sai anyi magana ki nuna kin fi kowa sanin Allah. to ni dai na faÉa miki ina son haihuwa, so na ke na ganni da Æ´aÆ´a, idan ba za ki haifa min ba kuma ki sanar da ni. kullum burina ne inji an kira ni da Baban wane, na dawo gida inga Éana ya tarbe ni, to kar ki sa nima na fara zargin wani abun kika sha saboda kar ki haihu, in ba ki haifa yanzu da Æuruciyarki ba sai kin tsufa kenan?, wannan ai ni kikawa mugunta ba kanki ba, shekara nawa haba".
Na Éago a gigice ina kallonsa, cikin sarÆewar murya na shiga ce masa,"haba Hubbi! haba!, ta ya kaima zaka shiga sahun masu tuhumata akan rashin haihuwa, kar ka fita daga imaninka mana, kar ka zama me shiga hurumin ubangiji, Hubbi akan me zan maka mugunta in sha wani magani saboda dai kar na Éauki ciki?, cikinka fa Hubbi, shin ka manta irin tsananin son da na ke maka ne".
Na tsagaita yayin da na ke goge hawayena, zuwa lokacin kuma kuka yaci Æarfina, kallonsa na ke yi ta ruwan hawayen da ya taru a idona.
"bayan iyayena kafi kowa sanin wace ni, kai zaka bayar da shaidar yanda na ke son yara, tun farkon aurenmu ka san da cewa ina bala'in son ace na haihu, na san kaima yanda ka ke son Æ´aÆ´a tun kafin aurenmu, Hubbi in ace da yanda zan yi in sanya cikin da zan haife maka a cikina wallahi tallahi da duk in da ake samo ciki sai na samo na saka, to amma ya zan yi, lokacina ne bai yi ba...".
nayi shiru ina Éago ido na kalle shi, ba ni ya ke kallo ba, idonsa na manne a Æasan tiles, hannunsa dunÆule a gefen bakinsa, yanayinsa na nuni da cewar hankalinsa sam bama akaina ya ke ba, ya nutsa ne can cikin tunanin wani abun.
na daÉa matsowa kusa da shi, kaina na kwantar a kafaÉarsa, hawayen idona ya sauka ta gefe ya tsarga ta cikin rigarsa, na danne kukana, muryana ya washe wajen ce masa,"na san Éazu da muka je asibiti gwajin haihuwa aka yi min, sun kuma bamu sakamakon gwajin nan, Hubbi don me yasa ba zaka faÉa min ba domin in san menene matsalatar, idan ta neman magani ce sai mu nema kaman yanda Iyam ta ce, idan ma wata mafitar za'a nema sai a nema, ba zan taÉa Éaga hankalina ba