bata da uba. damuwar da na ke ciki sam ba zata barni Éauko waya in daddana ba don Éebe min kewa, ga tarin tambayoyi sun cika ÆwaÆwalwata, ko canjin Hubbi bai girgiza ni ba kamar canjawar Iyam a gare ni.
kusan tsawon minti biyar Ummaa ta fito daga Éakinta, ganina zaune ta saki baki tana kallona da mamaki.
"Sa'ida zuwan yaushe?".
Ina murmusawa na ce,"zuwanmu babu daÉewa kenan Ummaa, Ina yini".
"Lafiya lau, to kuma kika zauna ke Éaya anan kamar wata baÆuwa, ruwan da aka yi da magribar nan ne yasa duk muka wuce Éaki da wuri, ke Éaya ce ne?".
Nace,"aa tare da shi muke".
"to Æalau dai ko?".
Na amsa da,"Æalau Ummaa, mun fita ne dama sai muka biyo ta nan Éin mu gaishe ku".
"Allah sarki, Nazifin bai shigo ba ne?".
"A'a yana Éakin Iyam, yanzu na fito a Éakin nima ina jiransa ne zamu tafi".
"bari na leÆa ai ban san kun zo ba, ina nemansa dama".
Ta faÉi hakan tana min wani kallon hadarin kaji. Éakin Iyam ta wuce ta barni da bin bayanta da kallo, miÆewa nayi na nufi Éakin Gwaggoje, tana kwance bacci har ya fara Éibarta jin maganata yasa tayi saurin tashi tana min sannu da zuwa. na zauna muna ta hirarmu da ita, har tana tsokanata wai bamu iya zuwa ba sai dare kamar wasu korarru, ko da ike wataÆila tuwon gidan muka biyo, ni dai dariya kawai na ke yi. sai kuma ta hau min hirar zuwa Æauyen da zata yi Æarshen wannan watan, tana cewa Æila ma tare zamu je tun da su Asama'u suma duk za su je, mijin Aina'u ne dai boÉararre ya hanata. shirin siyasar kano da aka fara yasa ta maida hankalinta ga radiyon, aifa nan ta fara tsinewa shuwaganni, idan na ce ta daina sai ta Æara tunzura tana akan me ba zata tsine musu ba duk sun sanya talakawa cikin wani hali, yanda ta haÆiÆance yasa nayi shiru ina dariya Æasa Æasa.
Sallamar su Iyam ce ta katse maganar da muke yi muka Éago idanuwanmu kansu. Iyam ta shigo tana cewa da mahaifiyar tata,"ai kamar na sani nace bara in leÆo ba lallai kin saki net ba".
Gwaggoje ta Éata fuska bata ce da ita komai ba, Iyam kuma ta shiga sauke mata net Éin. Hubbi ya zauna suna gaisawa, har yana tambayarta ita babu wata matsala a Éakin nata, ta ce da shi babu matsalar komai, ta faÉa tana saka masa albarka.
Wajen Æarfe goma muka yi haramar tafiya, lokacin ne kuma Iyam ke cewa da Hubbi.
"Ka kuwa ji haihuwar matar Nasiru?".
"Ahh matar Nasiru ta Æara haihuwa, lallai ne amma kuwa kinga bai kira ni ba wallahi, Allah ya raya".
Ta ce,"wallahi dai kaga su matansu sai haihuwa suke yi, ga su nan kowanne da yara uku biyu, kai ne dai shiru har yanzu, ban san menene matsalar ba, kai Éin dai lafiyayye ne na san Éan da na haifa, amma ya kamata ita ka kaita asibiti a dubata, ai ba a zauna shiru haka ba ayita zuba ido wa tsammanin da ba tabbas".
a hankali yace,"haka ne zamu je Éin in sha Allah".
Da sauri ta cafe,"Shalele ba fa batun wani in sha Allah ba, da zafifi ake bugun ice, in ba'a san abin yi ba yanzu shin sai yaushe?, rayuwar nan fa tafiya take tayi, girma ne ya ke daÉa kamaka, kana so ka mutu ne baka bar Éan da zai ke maka adu'a ba, haba ai ka samu ganin jininka ma a duniya rahma ne".
Sai kuma ta juyo gare ni tana cewa,"kuma ke Sa'ida ba ki sha wani abu ba da zai hanaki Éaukar ciki ba?".
Kaina a Æasa nace,"ban sha komai ba Iyam, amma ai mun je...".
Hubbi yay saurin tarar maganata da cewa,"Iyam bari mu wuce na bar baÆo zai zo ga kiransa naga yana shigowa".
Wani kallo tayi masa da cewa,"tana magana kuma ka katseta, ko wani abun ne baka so na sani?".
kansa Æasa yace,"a'a fa ita ai tana maganar mun je wajen wani me magani Éazu to bamu sami ganinsa ba, dama ina so sai mun gansa Éin sai kiji komai".
"To ai shikenan Allah ya kyauta, sai ku daure ku Æara zuwa amma kuje da wuri tun da irin su jama'a yawa suke musu. Gwara idan haihuwar ce bata yi muji da wuri ai ba'a ta zama haka ba, sa'anninka dai duk gasu nan da Æ´aÆ´ansu, kuma in jin daÉin rayuwar nan ne dai ai ka fisu, dukiya gata nan bata wasa ba, kaima in kana ganin yaronka ai sai kafi farin ciki da kwanciyar hankali, ga shi nan yanzu naga duk ka rame, kuma na san ba zai wuci damuwar rashin haihuwar kasawa ranka ba".
ta fuskanto ni ta ce,"ko cikin danginku akwai masu matsalar haihuwa ne Sa'ida irin wanda basu taÉa haihuwa ba haka?, kin san akan yi gado, kuma auren irin waÉannan cuturwa ce ga namiji ba kaÉan ba tun da an yaudare shi ba'a faÉa masa ba, amma dai ko me ke nan ki samu ki faÉawa iyayen naki a nema miki magani ba'a ta zama haka ba, kinga shi mijin naki hidindimu sun masa yawa ba ya ta fama da na magani ba tun da babu tabbas Éin ma za'a sami abin da ake so, dole dai iyayen na ki sai sun miÆe tsaye sun taimaka miki, abubuwa sun masa yawa shi kam, ga hidimarmu ga taki ta yau da kullum...kuyi magana da Ummar taki, nima Æ´aÆ´an gabana yawa gare su da sai inji da ke, to ba zaune na ke ba kullum cikin nemar musu tai