NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 17 of 97

i ba fa, ku fara biyawa ta wurinsa, ɗazu ma da ƙyar ya iya zuwa asibiti duba yaron da ka bige...yauwa Nazifi kaga anata mantawa, AC ɗin falon nan da fankar ɗakin Gwaggoje sun lalace, ita ma Ummaa naji tana akwai gyara a ɗakinta". Ya ce,"tom shikenan za'a gyara da wuri in sha Allahu". "Madallah Allah yay muku albarka, ya ƙara maka buɗi da wadata ko don taimakawa ahalinka da ka ke yi". Sashin Malam mu ka wuce, ina saka ƙafata a falon sai kuwa ƴan yaran su ka taso kowannensu da murnar yana faɗin,"oyoyo ga Anti Ca'ida". Su ka cukwikwiye ni sai farin ciki su ke da ganin nawa, Lubabatu ce me cewa da su,"ba za ku ƙyaleta ba sai kun yar da ita". "Ni dai ce matar Yaya kayami ta bani biccit zan caketa". cewar Sahura ƴar gidan Anti Aisha, cikin muryar gwarancinta me abin dariya. Abasiyya ta ce,"ai ko to duk wanda bai rabu da ita ba ba za'a ba shi abin da aka siyo ba, tun da duk ba ku iya gaisuwa ba". da saurinsu su ka sakeni kowacce na gaishe da ni cikin maganarsu ta ƴan koyo, da yake cikinsu duk babu wacce ta haura shekara biyar, Mansur ne ma da ya ƙara wayo kwanan nan maganarsa ke fita sosai. Shigowar Hubbi falon kuma duk sai suka yi kansa, dama shi gwanin son yara haka ya tarbesu da fara'a yana ba su hannu su tafa. Malam ya fito daga cikin ɗakinsa muka gaishe shi tare da yi masa sannu da jiki, yaji daɗin zuwan namu kuwa sosai, nan aka ɗora hirar da ake yi da mu, Amarya ta kawo mana abinci, ni dai na ce ta haɗe mana da su Lubabatu mu ci tare, dama shi Hubbi bai tsaya wata wata ba ana kawo masa ya tankwashe ƙafafu ya shiga ciki, da ike ma'abocin tuwan masara miyar kuɓewa busashshiya ne. Bayan mun gama cin abinci mu ka miƙe don wucewa, kamar kullum in muka zo Malam yay mana nasihohin da ya saba, da ƙara bamu tarin adu'oin da ya kamata mu riƙe a ko da yaushe musamman na tsari. mu ka yi godiya da adu'ar Allah ya ƙara lafiya sannan mu ka fito zuwa wajen Iyam. Can na baro Hubbi ya shiga ɗakin Yayan Shago. Shigata falon Iyam babu kowa, don haka na nufi hanyar ɗakin barcinta tun da banda shamaki da duk mallakinta, a hankali na murɗa hannun ƙofar na sanya ƙafafuna ciki bakina ɗauke da sallama. tana daga kishingiɗe akan ƙaton gadonta ta na kallon wani film a tashar gaskiyaplus, da ike ita ƴar gatan ɗanta ce tv biyu gareta falo da ta ɗaki. tun daga yanayin yacca ta amsa min sallama na sha jinin jikina, wani kallo kuwa da ta watsa min sai da na kusa kifewa a ƙasa, anan fa na ƙara tsinkewa da lamuran da suke ta faruwa. cikin mugun tsoro da shakkar yanayin fuskarta na ƙaraso ciki na durƙusa ina gaida ita, ba yabo babu fallasa ta amsa min gaisuwar tana miƙewa zaune yayin da ta ke gyara ɗaurin ɗan kwalinta. "Ke ce da daddare haka?". Da mamakin furucin nata na ɗago ido na kalleta, to sau nawa muna zuwa a lokacin da ya wuce haka ma, sai yau ne zai zama laifi?, sai kawai na sadda kaina ƙasa ina jan yatsu na ce,"tare da shi muke ya tsaya ɗakin su Adamu ne. mun sameku lafiya?". "Lafiya lau". ta amsa a daƙile ta na jifana da wani irin wulaƙantaccen kallo. Ledar da na shigo da ita na miƙa gabanta na ce,"ga wannan muka zo miki da shi". "Nazifin ne ya siya ko, na gode masa kuwa Allah ya ƙara buɗa masa, yaron ariziƙi irin albarka, haihuwa me gidan rana". ta ɗauka tana buɗawa don duba me ke ciki. Ni dai nayi shiru raina ina ta jin babu daɗi da yanayin yan da yau ta sauya min, ta fito da duk abin da ke cikin ledar waje tana ta sakawa wanda ya siyo albarka, yacca take faɗa da biyu don kusan magana ce take faɗa min, sai na ji duk na ƙagu ya shigo su gaisa mu tafi. "To wannan tufar dai ita zan fara ci, wannan yogot ɗin kuma ba in sanya shi firiji zuwa safiya yay sanyi sai yafi daɗin sha". Sakkowa tayi a gadon nayi saurin yunƙurawa ina cewa,"haba Iyam ina ɗakin sai kin je da kan ki, kawo na saka miki". Saurin janye ledar tayi tana yarfa min wani kallo, tana min harar ƙasan ido ta ce,"matsa ban wuri". Matsawa nayi ta wuce ta je ta saka abunta a firij, lokacin Hubbi su ka shigo shi da Adamu da Yayan Shago. ganinsa da tayi tamkar an tsundumata a aljannah, bakinta yaƙi rufuwa nan da nan ta shiga gyara masa wajen zama duk da cewa wurin a kimtse ya ke. gaisawa su ka shiga yi tana masa tambayoyi dangane da lafiyarsa da aikinsa, can ta waigo tana kallona ta ce,"ɗan je ki daga can babban falo mana, ai ba kya samu a gaba da kallo ba kamar wasu tv, hirar uwa da ƴaƴanta ai akwai sirri". Furucin nata ya taɓa ni, na miƙe jiki a saɓule na fita idona duk ya cika da ruwan hawaye, yaran dai har yanzu suna wajen Malam don ina jiyo ƴar hayaniyarsu, ƴan matan kuma suna ɗakunansu sai dai ba na je ba su tsammaci faruwar wani abun, idan na zo na saba a ɗakin Iyam na ke yini, duk mai son hira da ni sai dai ya sameni acan. ni kaɗai na zauna nayi jugum kamar wata marainiya wacce bata da uwa
🏠