iyata na Æissima min wasu abubuwan, emergency ward muka je, ashe da gaske ne yaron ya bige, ai da ya faÉa min ce na ke ya faÉi hakan ne kawai don ya kare kansa. Kuma Allah sarki yaron Æarami ne ya sha jiki don har karaya ya samu a Æafa, sai dai jinin ma da Hubbi ke cewa zai bayar an samu wani Æanin Baban yaron zai bayar. Mun Éan jima kafin mu yi musu sallama, suna ta godiya kuwa kamar yawun bakinsu zai Æare, ni ban sani ba ma ashe kusan kowa ya zo a Æ´an gidan su Hubbi, uwar yaron har da hawayenta wajen yi min godiya wai mijina mutumin arziÆi ne.
A can asibitin da muka je aka min test muna zuwa ya karÉo result Éin, ya jima a ofishin likita kafin ya fito, ni dai tun da ya fito na kalli yanayin fuskarsa naji jikina yay sanyi, na nemi sukuni na rasa, hankalina duk ya tashi, ko magana bai yi min ba yay gaba na bi bayansa. Motar ma yacca ya figeta ka ce wani bala'in yaÆi za'a yi, da haka muka baro asibitin ni dai na kasa magana kuma maganar na ke so in yi, shi kuwa kana kallonsa zaka san cewar ransa babu daÉi kwata kwata.
Lokaci Éaya idona ya cika da ruwan hawaye, ba'a faÉa min gwajin da aka yi min ba, haka kuma ba'a faÉa min sakamakon da aka samu ba, amma tuni zuciyata ta gama raya min abin da sakamakon ya bayar, shikenan tawa kuma ta Æare, ta tabbata da gaske bana haihuwa, yanzu cikin wannan tsananin halin wa zai rarrashe ni?, madafar da na ke gani in ji daÉi yanzu bata ni ya ke ba, fatana Éaya kar aurena ya dagule ta silar hakan.
hijabina na saka na goge hawayen da ya sakko min, Allah kaÉai ya san me na ke ji a zuciyata, yanzu shikenan har in koma ga mahallicina ba zan ga jinina ba?, ba zan haifi yaron da zai kalle ni ya kira ni da mahaifiya ba?, zan mutu ban bar wanda za'a ke gani ana tunawa da ni ba in ci arziÆin adu'a ta dalilinsa, shikenan duniya ba zata kira ni da sunan uwa ba?.
Æwarai na san an buÉe min babin Æalubalen dangin miji na tsantsar cin mutunci da gori akan rashin haihuwa?, canjin matsayi a wurin miji?, Æarin aure ya tabbata lahu na sani, don haka dole ne cin zarafi daga kishiya, wani sabon kuka ya zo min, na kifa kaina a saman Æafata ina rera shi a hankali, na sani tabbas duk wani abu da zai samu bawa daga Allah ne, kuma hakan alkhairi ne a gare shi, fatana Éaya ubangiji ya ba ni ikon cinye wannan jarabawar rayuwar.
Ina cikin kukan na jiyo muryarsa yana faÉin,"wai ke babu ranar da za ki girma ne?, kina wani kuka sai kace jaririya, mene hakan?, ba'a miki komai ba ki kama kuka, wannan ai shirmen banza ne".
Na Éaga ido ina kallonsa, gaba Éaya babu wani tausayina a saman fuskarsa, balle a biyo ga batun rarrashi da ban haÆuri da nasiha, dama tuni ya saka hijabi a tsakaninmu kan waÉannan abu ukun. ba a komai ne ka ke da buÆatar ayi maka bayani ba, wani abun hankalinka da tunaninka zaka sa ka fahimta, tsawon watanni ban san matsalar da ta kawo canjin yanayin zama tsakanina da shi ba, amma daga abin da Yayarsa ta zo tayi min jiya na Éora samun saÉaninmu da shi akan hakan, don na san dai tabbas in har laifi nayi za'a faÉa min, shi mutum ne dai baya Éoye wannan. hmmm Æwarai na sani yanzu zan shiga wata sabuwar rayuwa ne, ba fata na ke wa kaina ba, amma na sani na gama rayuwar farin ciki a gidan aurena, domin banga alamun Hubbi zai karÉi wannan Æaddarar tawa ba, banga alamun zai taya ni mu cinye jarabawar tare ba, lamarin zai zama tamkar ni na gaza ne.
Muryata gwanin ban tausayi na ce masa,"Hubbi ba ka faÉa min abin da likitan ya ce ba".
"ke kika kawo kanki?".
"Ba ni na kawo kaina ba amma kuma tawa lafiyar aka duba ai, ina son sanin abin da likita ya faÉa kaji, ina son sanin abin da yake damuna".
Maimakon amsar tambayana sai jan tsaki yay. a maimakon gida sai naga mun Éauki hanyar gidansu, haka kawai kuma a karo na farko naji ina tsoron zuwa gidan, daga waje ya ajiye motar bamu shiga da ita ciki ba. Ni ya bawa ledar siyayyar da mu ka yiwa Iyam, ginin gidan irin ginin tsakiyar nan ne, babban parlo zaka fara shiga, a ciki kuma kowa da Éangarensa ta can ciki. shigarmu falon mu ka tarar da Amarya, tana ganinmu fara'a ta wanzu a fuskarta tana tafa hannu wajen yi mana lale lale.
Nayi Æarfin halin Éoye damuwata na aro jarumtar fara'a da walwala na yafa. na duÆa Æasa na gaisheta daga bisani kuma su ka shiga gaisawa da Hubbi. nan yake cewa da ita,"na ji gidan tsit".
Ta ce,"umm suna can falon Malam ana hira".
"Iyam ma tana can?". Ya tambaya a lokacin da yake cire hularsa yana susa.
"anya kuwa, kamar dai tana Éakinta".
sai kuma ta dube ni tana cewa,"kin san bamu jima da gama hirarku ba, na ke cewa ya kamata in samu lokaci in shiga in duba ku, ashe ma kuna tafe a hanya. to fatan dai duk kuna lafiya".
Ina murmushin yaÆe na ce,"muna lafiya lau, ya muka same ku?".
Ta ce,"lafiya lau. Tashi ku shiga ciki nima zan Éaukowa Malam abincinsa ne".
Hubbi zai wuce ta dakatar da shi da cewa,"Malam yini yay yau bai ji daÉ