NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 14 of 97

har ta firgita Jamil, nan kuwa ya tsanyare da kuka, na furta na shiga uku ina jijjiga yaron a kafaɗata, na kalli Hubbi da idanuwansa ke a warwaje nace,"don Allah kayi haƙuri". Ya watsa min banzan kallo da ya saka yanayina sanyi, na sadda kai ƙasa ina mayar da ruwan hawayen da ke shirin sakkowa. A hankali nace da shi,"don Allah kayi haƙuri kayi ƙasa da muryarka kaga bamu kaɗai ba ne a gidan...". Ni dai ban iya ƙarasa maganar ba kuka ya ƙwace min, ƙafafuna na rawa na nemi kujera na zauna don sam bana so in fita a haka Hassana ta fuskanci matsalar da ke tsakanina da mijina. Ganin na zauna takaici ya kama shi ya kuma doka min tsawa da cewa,"dukanki nayi ko zaginki nayi da za ki sakar min kuka?". Sai kuma yaja tsaki yace,"ki wuce kije ki sallameta ta bar min gida, minti biyar na ba ki ki shirya zamu fita". Saboda yanayin yanda na ga ya rikiɗe nayi saurin miƙewa jiki na ɓari, Allah yasa ta cikin ɗakinsa akwai ƙofar da zata sadaka da saman bene, don haka nabi ta nan gudun kar in fito in haɗu da Hassana. Har na shiga ɗakina Jamil na ta kuka ina aikin jijjiga shi, wanka na yiwa yaron na saka masa wasu sabbin kaya da na siya nacl ce zan kaiwa Maman Amatu kayan barka. ai kuwa kamar jiran wankan yake ina gama shirya shi yay bacci, nima shiga nayi na ɗaurayo jikina na zo na ƙara shiryawa cikin dogowar riga coffee colour, na ɗauko hijab ɗina yadi uku da rabi na saka sannan na ɗauki liƙab na zura a jakata. Ko da na sakko na sami Hassana tana jirana, galala tana kallona ta ce,"wai bacci yaron nan yayi?". Ina murmushi na ce,"bawan Allah shima ya gaji, kuka ya saka ina masa wanka kuma sai bacci". Ta karɓe shi fuskarta sai ƙara fidda annuri take yi tana ta godiya da yaba kayan da na saka masa. Tana ce mun za ta tafi nayi shahadar ce mata,"a'a ai ki tsaya kawai mu fita tare sai mu rage miki hanya, kema ai sauƙin ki ne". Bata ƙi ta tawa ba cikin jin daɗi ta ce,"aikuwa na gode sosai, dama yanda yamman nan tayi sai kayi ta fama da masu ɗan sahu". Na juya ina ce mata ta jira ni gamu nan fitowa, haka na wuce gabana sai dukan tara tara yake, tsorona bai wuci inje in ce masa zamu ragewa Maimuna hanya ba ya yarfani, yazo yay ta ɗaga murya yana hayagagar faɗa har mata ta jiyo mu, ni ban ma san shegen karambanin da ya kaini ce mata ta tsaya ɗin ba. Yana ɗaura agogo na same shi, yayi kyau sosai a baƙin yadin da ya saka, lokaci ɗaya sai naji tarin tsoro da shakkar da su ke manne a zuciyata sun bi iska sun tafi, na taka na isa gabansa, ba tare da sanin ma shigowar tawa ba sai ji yay na kama hannunsa ina karɓan agogon in ƙarasa saka masa, haka maɓallin gabar rigarsa ma na saka masa sannan na miƙo masa hularsa ya saka da kansa, don ita duk san da zan saka masa sai yay min tsiyar Habibty in kika sa min hula sai ki mayar da ni kamar wani tsolon rake, ga shi kin kasa ɗaukan darasin da na ke miki akan yanda ake sakata. To yau dai bai tanka min ba, kallona kawai yay na ƴan sakanni ya ɗauke ido yana wucewa ya ɗauko maƙullin mota. Sai a sannan na sami zarafin ce masa,"Hubbi don Allah zamu wuce tare da Maimuna mu sauketa a hanya". Na faɗi hakan ƙirjina sai bugawa yake yi. "to". gaba nayi yana bayana, sai da zamu fita a ɗakin naji yana cewa,"wannan hijabin ne kawai da ke?". Na juyo na kallesa na kalli ƙasan rigata da yake kallo wacca adon stones ɗinta su kai bajau, in dai mai idanu ya kalla sai sun ɗauki hankalinsa, dalilin hana ni saka ƙaramin hijab kenan idan na saka kayan da adonsu ke bayyana har can ƙasa wanda zai ɗauki hankali da ban sha'awa. Muryata sanyi ƙalau na ce da shi,"wai bai wanke sauran ba sai waɗannan kawai ya kawo min, ina ta jiransa ma jiya shiru bai zo ba ban san uzurin da ya riƙe shi ba, ko na makaranta ma bai kawo min ba". Wayarsa ya zaro ya danna kiran lambar me wankinmu, yana ɗagawa ya ce da shi,"kana ina?". Ban san me Shehun ya ce masa naga ya sauke wayar yana tsaki. Kuma duk yanda aka yi uzurin da ba zai iya da shi ba ne shiyasa ya haƙura dole, banda haka ce zai yi da shi a ko'ina yake ya kawo kayan yanzu, fitar ma naga ya ɗaukaketa ne amma banda haka akan na fita da wannan hijab ɗin na jikina gwara mu fasa zuwa, ko kuma mu jira ko ƙarfe ɗayan dare ne Shehun ya kawo sannan mu fita. Wani daɗi naji da yanda naga ya sakarwa Hassana fuska, kaman ba shi ne miskilin kwana biyu ba, cikin mutuntawa da girmama juna suka gaisa har da kansa yake bata haƙuri akan rashin zuwana barkan haihuwan Jamil, na kuwa ji daɗi sosai don ni kunya ma sawa tayi na kasa ce mata komai game da hakan. Har muka fito farfajiyar gidan suna ta maganganunsu, yana tambayarta amma dai ba yau ne zata wuce can Wudil ɗin ba, ta ce ai mota babu wuya tana zuwa tasha zata samu motar da zata ta shi. Haka muka baro gida, ya sauko kamar ba shi ba, wanda nayi mamakin hakan matuƙa, yanda bana so Maimuna ta fahimci akwai matsala
🏠