NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 13 of 97

nan kuma ni Hassy menene shi, haka fitilun falo ma wai ai ita ba zata iya kwana ba gani zata yi kamar zasu faɗo kanta taga haka ake yi a film ɗin indiya...cikin hirarmu take bani labarin mutuwar mijin Firdausi itama ƴar group ɗinmu ce a makaranta, na ke ce mata wallahi ban sani ba amma zan samu in shiga a satin nan in mata ta'aziyya. Hirar tamu kuma ta juya kan kasuwancin da uwar bari tasa mata su ka durfafa, har take neman shawarata akan sana'ar da take so ta fara na kiwon kifi, ai kuwa nan na ƙarfafa mata gwiwa akan tayi ɗin na kuma daɗa nuna mata muhimmancin sana'a a wajen mace. Taji daɗin shawarwarina sosai, mu ne har la'asar anata zuba ana shewa, sai lokacin ne tayi ɗan jim ta kalle ni tace,"don Allah kiyi haƙuri da tambayar da zan yi miki". Nace mata,"tambayan me Hassana?". Ta numfasa tace,"kiyi haƙuri ba sa ido ba ne, damuwa da ke ne wallahi, ke dai kin san yanda Allah ya jarabce ni da sonki, domin ni ba matsayin ƙawa kike garen ba, ganinki na ke tamkar Hussaina da na saki Nono ta kama". Na murmusa kuncina na ce,"na sani Hassana kar ki damu faɗi abin da yake cikinki". "Me yake damunki naga kinyi uwar rama haka?". "Wai da gaske ramewa nayi?, Sai aita na rame ni kuwa banga ramar da nayi ba, Hubbi ma ce yay nayi ƙiba". Galla min harara tayi tana faɗin,"ban sani ba ƴar rainin hankali, ga fa ƙashin da ke wuyanki Sa'ida abin da babu a da". Dariyar da ta bayyanar da haƙorana na yi nace mata,"kar ki damu ba wata damuwa ba ce, jinya na sha kwana biyun nan, watana biyu a kwance". Aikuwa ranta ya ɓaci ta nuna min rashin jin daɗin hakan. ta fara mita akan me yasa ban taɓa faɗa mata ba, ta ya za'ai ace har na sha jinya irin haka bata sani ba, ko bata zo duba ni ba adu'a da sannu ai suna da daɗi. Ni dai haka nayi ta bata haƙuri, ta gama mitar sai kuma can ta doka tsalle ta rungumoni tana murmushi cikin fara'a tace,"kinga ki bani wanga albishir kawai kar ki ja min rai". Nayi lakato ina kallonta domin na san in da zancen nata ya dosa, ta zame a jikina tana daɗa cewa,"wata nawa?". Na waro ido na ce,"keee mene wata nawa?". Tayi min wani kallo na kar ki raina min hankali. Na ce,"Allah kuwa, idan shi ne ai tun a waya zan sanar miki, wallahi bani da komai Hassana har yanzu shiru, sai dai a ci gaba da samu cikin adu'a". Jikinta a sanyaye tace,"to Allah yasa jinkirin Alkhairi ne. Amma dai ai ba kya fuskantar wata matsala ko, kin san sha'ani na dangin miji". Murmushi nayi na ce,"ko ɗaya fa, ai kin fi kowa sanin surukai na. Ita Iyam ma da kanta take nema mana magani". Tace,"Allah sarki. To Allah yasa a dace, ke kam Sa'ida ai kinyi dacen suruka wallahi, ga dangi miji kamar kece ƴar tasu". Ni dai murmushi kawai nayi na kuma san yanda nayi na katse maganar haka. ta miƙe tana faɗin,"bari nayo fitsari in zo in ɗauki hanya yanzu za kiga magriba tayi". Tashinta ba daɗewa naji Maganar Hubbi akaina yana cewa,"ina jiranki". Bayansa na bi da kallo wanda tuni ya wuce yay komawarsa ɗaki, nayi godiya ga Allah da yasa Hassana bata nan, da haka zai fallasa lamarin da na ke ɓoyewa. Kaina na girgiza cike da takaici da baƙin ciki na tashi, na ɗauki Jamil na tafi da shi. A ɗakin na same shi yana kaiwa da komowa, na tsaya daga gefe na ce,"gani". Tsaye yayi yana ƙarewa Jamil kallo, ban sani ba burge shi yaron yay kome masa ne oho, yana dai ta kallonsa kamar ma zai miƙo hannu ya karɓe shi. shirunsa yay min yawa na ɗago kaina na kalle shi naga bai ɗauke ido daga kallon Jamil ɗin ba, muryata a hankali na ce masa,"ɗan gidan Hassana ne". Sai sannan ya ɗauke idonsa akan yaron yana cewa,"wace hakan?". Na kalle shi nayi guntun murmushi na ce,"Hassana Tijjani dai ƴar ajinmu". "Ohhh, haihuwa ta ƙara yi?". "Ehhh shi ne wanda aka haifa ranar da zaka tafi Hajji ban samu zuwa barka ba". Ya sake cewa,"ohh Allah ya raya". Na amsa da,"amin". jimm na ƴan sakanni kuma sai ya sake cewa,"ashe Yaya ta zo jiya". Furucin nasa yasa gabana ya faɗi ras, duk sai na nemi na daburce da yay maganar wacca ta fama ciwon jiya na cin mutunci da Yaya ta yi min. Idona na rumtse gam nace,"ehh na manta ne ma ban faɗa maka ba". Cikin fusata ya ce,"wai ke mene matsalarki ne, iskanci ko kuma rashin mutunci?, Yayan ta zo jiya, jiyan ma da daddare amma saboda rainin wayo za ki buɗi baki kice kin manta da zuwanta. dama har haka kika fara raina min ƴan uwa?, Ashe maganar da na ke ji na cewan kina wulaƙanta su gaskiya ne ba ƙarya ba, to bari kiji na faɗa miki, zan iya ɗaukan komai amma ban da cin zarafin ƴan uwana, ba zan ɗauki hakan ba Sa'ida ke kin san waye ni, akan ƴan uwana ina iya rabuwa da kowa ko da ace ɗan cikina ne...". Furucinsa na ƙarshe yasa na kalle shi babu shiri, ɓoye raunina nayi na tari numfashinsa ina basa haƙuri, saboda yacca yake ɗaga murya tsab Hassana da ke falo zata iya juyo komai. Daka min tsawa yay wacca
🏠