NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 12 of 97

ya gagara ya sanar da ni, sai kuma kawai na bagarar nace,"Allah ya ƙara sauƙi". Yace,"amin, ya zubar da jini da yawa yau zanje a ɗibi nawa a saka masa". Kallonsa nayi ta ƙasan ido nace,"Allah ya taimaka". Ina faɗar hakan na bar masa ɗakinsa na fita. Samu nayi ana ƙwanƙwasa ƙofan falo, na ƙarasa na buɗe, ganin wadda ke tsaye a gabana nace,"Hassana Tijjani". Na faɗi sunan nata da muryar bayyana murna da jin daɗin ganinta. hanya na bata ta ƙaraso ciki tana ta nishi alamun ta gaji da yawa, jakar hannunta ta wancakalar kan kujera tare da kwance goyon bayanta, sannan tace da ni,"me gidan yana nan?" Nace,"Yana ciki". sai ta fasa cire mayafinta tana sake cewa,"ke ƙaro gudun Acn nan, jina nake kamar a garwashi". Na wuce wajen makunnin AC na ƙaro ina cewa da ita,"daga ina kike haka ne?, Naga sai zufa kike haɗawa...bari na kawo miki ruwa". Kitchen na wuce ina jiyota tana faɗin,"ke dai bari tafiyayya nayi tun daga Shanono, naje gidan wan Mamarmu gaisuwar ɗansa, muna shigowa kano kuma muka wuce gidan ƙanwata Saratu anyi mata tiyata an ciro yaro babu rai, nace dai to yau tun da Allah yasa nayi kusa da unguwar su Sa'ida in sha Allahu sai na zo mun gaisa". Ina ta murmushi na ajiye babban farantin hannuna da na sako ruwan sanyi da lemun ɓawo da ayaba,"sannu da hanya, to ya aka yi kika gane gidan?". Tana goge zufa tace,"na kira wayanki ban samu ba sai kawai na kira Ummani ta min kwatance". Nace,"kar ki ce min sai da kika je gidanmu". "Wallahi sai da naje, ai ba zan iya zuwa kano dai in yawace yawace ban je na gaida Ummani ba, tace ma in gaida ke". Na kuwa ji daɗi matuka da cewarta, fuskata ta washe da annuri ina cewa,"Maimuna ina godiya da yanda kike girmama mahaifiyata, Allah ya bar zumunci". Ta amsa da amin, ni kuma na ƙara cewa,"ya ƙarin haƙuri?". "haƙuri mun gode Allah, kwanakin nan anata rasuwa wallahi, rasuwar ma ta matasa". Nima cikin jajantawa nace,"wallahi kuwa sai fatan Allah yasa muyi kyakykyawan ƙarshe. Dama Saratu lokacin haihuwarta yayi?". "Ina fa bakwaini ne, to ɗan ma sai yazo babu rai". Nace,"Allah sarki Allah ya bada rayayya". Naje na ɗauki yaronta da ke bacci na kwantar da shi kan wata ƙaramar katifa da na ɗauko gudun kar yay fitsari akan kujerar. Ni dai har raina naji daɗin ganinta, rabona da ita tun kafin mu dawo gidan nan, ƴar ajinmu ce tare muka yi sakandire, tana cikin abokan arziƙin da aka yi zaman mutunci da su, ƴan gidanmu kaf babu wanda bai san Hassana Tijjani ba, kafin muyi aure yawan lokuta ta kan zo gidanmu, bini bini ta kira Ummani su gaisa, saboda tana sonta sosai, ko ina ta shiga ta yabi mahaifiyata taita bada labarin mutuncinta. duk da ni ina ɗan shashshareta saboda ban cika son ƙawaye ba, amma hakan bai sa ta ja baya da ni ba, ko da bikina tun daga Zariya ta zo sai da ta kwana uku, haka da su ka dawo zama kano ta jajje gidana ba zai ƙirgu ba, amma ni kuwa tsabar kirkina zuwana gidanta bai fi sau uku ba. "Sa'ida ban fa yi sallah ba. In fara yi kafin mu zauna wannan hirar tamu ta yaushe gamo". Ta ce bayan ta ajiye jarkar ruwan da tun da ta kafa kai bata sauke ba sai da ta kusa shanyewa. Na kalleta murmushin fuskata bai ɗauke ba na ce,"to ko sama zamu hau, kyama yi wanka kiji daɗin jikinki". Tana dariya tace,"wanka Sa'ida kamar wacca ta zo kwana, raba ni, na dai yi sallar kawai. Sallar ce in baka yita ba babu natsuwa kwata kwata". Tashi nayi na ɗauki yaron nata da na ke ta jin kunyar in tambayeta sunansa, lokacin da ta haihu har hotonsa ta turo min da sunansa, haihuwanta biyu duk babu wacca naje mata barka, amma hakan baisa ko kaɗan Hassana ta nuna min rashin jin daɗinta ba ko ƙorafi, ita ce ma mai yawan nemana a waya taji ya nake. Ina nufar sama ta ce da ni,"Sa'ida ku fa gidan nan na ku na ƴan gayu ba a rasa ku da banɗakuna a ƙasa, saboda haka ki taimaka ki rabani da hawa dogon benen da idanuwana ke gani, ba za ki gane yanda ƙafafuna su ke a gajiye ba". Gajeriyar dariya nayi na maida yaron na kwantar, bedroom ɗina na ƙasa na rakata, sai da na takurata akan tayi wanka. Na fito na barta a ciki na wuce kitchen na haɗo mata kayan abinci, lokacin yaronta ya tashi na ɗauke shi ina ta masa wasa, yaron tubarkallah ɗan kuɓulɓul da shi ga shi tsab tsab, babu ko irin ƙarnin tumbuɗi a jikinsa sai ƙamshi yake yi, daɗina da Hassana kenan tsabta gaba ta bata ba baya ba. Dawowarta tana murmushin jin daɗin da ya kasa ɓoyuwa a fuskarta take cewa,"au Jamil tashi ya yi?". Aiko nan naji daɗin faɗar sunan da tayi, ina murmushin nima nace,"ai yanzu na ke cewa Jamil har haka yayi wayo sai dariya yake yi abinsa, ga shi babu ruwansa da rigima". Haka ta zauna ta shiga cin abinci, tana ci muna ta hira abinmu, sai zuba santin gidana take yi, faɗi take wannan ai shi ake kira da aljannar duniya, dama gata ƴar barkwanci duk in da na zagaya da ita sai tace wan
🏠