NOVEL SHARES -
taci gaba,"to ɗazu ma daga shiga ɗakin nace tazo ai ma ta allura sai ta balbaleni da masifa, wai na fita a lamarinta na daina shiga sabgarta ita bata son takura. jiya jiyan nan ma fa haka taje ta ƙala min sharri a wurin wancan ɗin, shi kuma sai ya turo ɗan'uwansa, haka Amadu yazo tsakiyar kaina kamar zai zaneni yayta banbami wai na daina takura mata...ka ga fa ba yau ta soma haɗani da mutane ba, kwanaki da nayi baƙi Allah yarinyar nan sai ta koma kamar marainiya a gidan nan, kaga waccan kujerar nan ta zauna ta dinga ɗacin rai da nurƙufanci tana kuka haka kawai ba'a ma ta komai ba, duk dai dan taja min masifa, su kuma da gulma suka dameta da tambayar wai me aka ma ta, to ka faɗa min Adamu duk san da tayi irin haka agaban iyayenta me za su ce tsakani da Allah, ai sai suce sun rufa mana asiri ni kuma ina tsangwamar ƴarsu. ka tambayeta kaji wallah ko bacci bana iyayi sai naga sunyi ita da ƴar'uwarta, amma ta rasa da me zata dinga saka min sai da mugun halinta, kuma da tayi abu nayi ma ta gyara zata turo baki gaba kamar kuratandu, to ni dai na gaji gwara na bar ma ta gidan, tun da dama ba Ummana bace ta siya".
Baba yace,"kiyi haƙuri Yagana ba zata ƙara ba daga yau". tace,"hmm Adamu kenan baka san wace Mairo ba...to ka bar lallamata ina faɗa maka, dan kaima bata ƙi taja maka baƙin jini ba a wurin iyayenta, kaga dai fa ba lafiya gareta ba amma taƙi tsayawa ai ma ta maganin abin, alhalin tasan yau Akila zata dawo, to yanzu idan ta dawo taga ba'a bata magani ba'a ma ta alluran da likitoci suka bada me shegen tsada ba me zata ɗaukemu tsakani fa da Allah?, to ni dai gaskiya asan abinyi, ko zamana a gidan nan ko barinta dan ni nagaji da halinta, ba zai yiwu ta dinƙa neman jefani a masifa ba". "kiyi haƙuri dai Yagana". "to haƙuri ai ya zama dole Adamu. kaga shi wancan ɗin da ka aika a kira tun ɗazu har yanzu bai zo ba, dama ni nasan ba zai zo ba indai yasan kana ɓangarena". Baba yace,"to wai shi da ba shi da lafiya ma, yaushe ya tsiri wannan halin?". maganar Baba ya ke ransa a ɓace. tace,"aini na gama magana, ga dai Zulai nan ka tambayeta kaji. Kabiru ai ya zama sai adu'a". Zulai tace,"aini Yagana duk ban san hakan tana faruwa ba. amma komai zai daidaita". tace,"uhmm daga jiya zuwa yau kawai Kabiru ya zama abin da ya zama, ki faɗa min idan akai gaba sai ya ya? aishi ice tun yana ɗanye ake taƙwarashi".
Ya Kabiru da Lukman su ka shigo, ya zauna a ƙasan carpet kansa a ƙasa. Baba ya shiga yi masa faɗa sosai shi kuma yana bada haƙuri. ya ɗaga kai ya kalli Yagana yace,"Yagana dan Allah kiyi haƙuri". tace,"na haƙura na yafe maka. nima kayi haƙuri ka yafe min". sannan Baba ya juyo kaina da nawa faɗan, faɗan da sai da ya sa ni kuka, na bata haƙuri kuma sai da ƙyar tace ta haƙura.
Baba zai fita nima na kai masa ƙarar Ya Kabiru, kuma bai tsaya ba yace,"wannan kuma laifina ne, may be rashin kunyar da nakewa Yagana nayi masa".
gaba ɗaya na manta da zancen za'a min allura sai bayan da taron kai ƙorafin Yagana ya ƙare, a rayuwata ganin allura na ɗaga min hankali, Ya Kabiru ya tashi zai fita nayi jikinsa na ƙanƙame shi ina kuka, kamar zai janyeni kuma sai ya fasa. ya ɗaga wayarsa da ke ƙara ya kara a kunne. daga yanda naji ya amsa maganar da aka masa daga cikin wayar na gane da ƙyar idan ba Ummina bace. "oak tom gani nan zuwa". sai kawai naji ya ɗora min wayar a kunne, muryasa can ƙasa a hankali yace,"Ummi ce". sai na shiga murna babu shiri, ina tambayarta yaushe zata dawo. abin da na sani kawai shi ne, naji san da Ya Kabir ya karɓi allura daga hannun Mu'azzam amma ban san ya tsira min ba har ya zare sai da Yagana tana lailaya min wurin. na kalli Yaganan nace,"allurar za'a min, nafa ji sauƙi". ta taɓe baki bata ce da komai ba ta wuce ta bar wurin.
ina Kallon Ya Kabir da zai fita nace,"Yaya tun shekaranjiya fa Ummi tasa aka kawo driver, amma kanata driving da ƙafanka bai gama warkewa ba". "who told you so?". na ɗan haɗe fuska nace,"ɗazu ai ka kai Nawwara makaranta". ya ɗaga kafaɗa sannan yace,"am well now. za ki je ɗauko Ummin?". nayi knodding kaina da cewan,"ehh". na faɗi hakan cike da murna, dan sosai nayi kewan Ummina. "to ki fito da sauri". ya faɗi hakan yana sa kai ya fita daga parlon. da ni da shi da Basma mu ka tafi ɗauko Ummi a airport.
for those who viewed, vote, like and comment i really apprciate, thank so much to you guyz, i love you lodi lodi.
*Plss Comment, Share & Vote.*
[7/16, 17:45] Halimahz(Anyway): *SIRRIN ƁOYE*
*©️Halimahz*
*Anyway@arewabooks*
*HalimaAnyway@Wattpad*
*Halimahz@Bakandamiyahikaya*
_Ina ƴan kasuwan da ke da buƙatar a tallata masu kasuwancinsu cikin littafinmu domin ƙara samun customers?, a sanka a san sana'arka, zamu tallata maku hajarku cikin farashi mai rahusa, ku dai ku tuntuɓi wannan number 08024976578(whatsapp only) kai tsaye, mai talla a ko da yaushe shi ke da riba._
*(43)*
*4Months Letter.*
*Qatar University, Doha.*
"Maryam Mukhtar Afafa". sautin kiran sunan nawa ya fito ta cikin hall ɗin daga ca