NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 167 of 223

katseta,"kai amma dai duk inda ɗan iska yake yafita daban, yanzu ke Adawiyya saboda babu tsoron Allah babu kunya a ranki shi ne kike maganar Suhail...to yanzu ni ko shegiya ce Adawiyya ai bana shige miki gaba ba akan wannan zancen sai dai na shige miki baya, to bada ni ba gaɗa a kabari, ni rashin hankalina bai kai intaha ba, kuma wallahi bari kiji yau ko Suhail ne yazo da batun aurenki gidan nan sai na shiga na fita al'amarin ya tarwatse, sai dai nima ku biyo min ta ƙarƙashin ƙasar amma wallahi ba zan bari wannan mai farar zuciyar ya auri macen da ta cutar da shi ba." ta ke ruwan hawaye ya cika idon Adawiyya tace,"haba Yagana karki manta fa ni wace ɗinki, abunda ya faru ya rigada ya faru sai dai a kiyaye gaba, nayi nadamar abin da na aikata kuma har yanzu dana sa ni nake...duk da cewar sun yafe mana amma wallahi har yanzu zuciyata ta kasa samun natsuwa, tabbas yanzu na yarda cewan duk wanda yay ƙudurin hana wani bacci to shi ne zai kwana bai bacci ba, dan Allah ki taimaka min, wallahi da tsarkakkar zuciya nake sonsa tun farko...kuma na rantse miki da Allah yanzu zuciyata fess ta ke akan kowa, Allah ya shiryeni ya ganar dani". "to Allah yasa anyi taubatun nasuha, amma wancan zancen naki kam tun muna ta daɗi da ke ki barni da shi, ki nemi wani a cikin manemanki kawai." Adawiyya tayi shiru tana hawaye, Yagana ta miƙe ta fita ta barta a wurin bata kuma tanka ma ta ba. a ɗaki ta sami Kabir zaune yana kallo shi da Aminu, ta kalle shi tana aikin taɓe baki for a while kamin ta juya ga Aminu ta amsa gaisuwarsa da cewar. "kai kuma yaushe kazo gidan?." "tun ɗazu na shigo Yagana." sai ta ƙara gwame baki tace,"yayi kyau, lokacin da Hajara ta rasu ta bar Yaranta ababen tausayi kishiyarta bugar ƙirji tayi tace babu ɗan da zata riƙe, sai ni Rakiya ce na raini Kabiru da Aminu da ƙarfina da jinina, yo a rayuwa kuwa ai bana zama abar a wulaƙanta ba tun da ance wanda yay maka alkhairi karka manta da shi...amma da yake Aminu kai ɗan halak ne har ka iya shigowa cikin gidan nan baka fara zuwa ka gaishe da ni ba, kai ai ga me ɗan'uwa tun da ba Uwarka a gidan ba wurin wanda zaka, wato da ban zo nan ɗin ba ma ba zamu sami ganawa ba." Aminu ya girgiza kai da cewar,"Yagana ni ɗin banzana in shigo gidan nan banje wurinki ba, wannan ma ai zance ne." tace,"haka ne, to ya wurin su Zannirar?." "su na lafiya." "to ka gaidasu idan kaje, ranar nan ai da na shiga wajejen naku na biya ta wurinta gidan a rufe, sai maƙwabciyarku ke ce min taje asibiti, to Allah ya raba lafiya". ya amsa da,"amin Yagana". Nawwara ta shigo parlon hannunta riƙe da kwandon abinci, Yagana tayi ma ta nuni da inda zata ajiye, bayan ta aje ta gaida Aminu sannan ta gaida Kabiru tare da yi masa sannu da jiki, ya amsa ma ta yana bin bayanta da kallo har ta fice daga ɗakin. daga inda ya jiyo ƙwafar Yagana ya karkatar da kai kaɗan ya dubeta yanda ba zata gane ba, yana kallon yanda ta ke aikin jijjiga kai sai kawai ya motsala leɓensa yaci gaba da sauraron labarai. sai da Yagana da Aminu suka gama hira sannan ta dawo kansa da cewar,"Baba kayi haƙuri ni bana gaba, ƴarka ce dai insha'Allahu ba zan kuma taɓa maka ba, dan haka ka sauka daga wannan dokin zuciyar ina mai bada haƙuri...ina yini, ya sauƙin jiki?". ya gimtse dariyar da ke neman kubce masa. "Baba magana na ke, kayi haƙuri dan Allah, a wannan halin da kake ciki ba zan iya ɗaukar shariyarka ba...kuma na maka alƙawarin Ƴarka Mairo ba zan ƙara takura mata balle har ta kuma ƙala min sharri akan abinda banji ba ban gani ba". tana yin shiru yace,"Yagana dan Allah Maryam ba Mairo ba". tace,"to Baba naji na ɗauka...yanzu dai ka haƙura ɗin ko?". ya kalleta yace,"na haƙura tsohuwa". "yauwa Baba Kabiru Allah ƙara maka haƙuri. ban sami leƙowa ba tun safe, sai nace Zulai tazo tayi maka gashin ai anyi ko?". "ehh anyi, yau ina jin daɗin jikin sosai...Ahmad ma nake jira ya dawo mu ɗan zagaya". "ehh ai da yake ya fita kai Ƴar taka yawon shaƙatawa, amma nasan duk inda suke su na kan hanya, Allah dai ya ƙara lafiya...ga tuwan dawar nan nayi maka lafiyayye, har man shanu nasa Mujibu ya aiko min, kaci sosai kaji ɗan albarka, bana son wannan rashin cin naka". "zanci Yagana bari ayi sallar magriba tukunna...tun yaushe suka fita?". yay tambayar yana jin wani abu na tokare masa ƙirji. "ah tun kamin azahar suka fita". sai ta karkata ga Aminu tace, "Aminu ai yau Allah ne yay da sauran kwanana a gidan nan". daga Aminun har Kabiru sai suka waro ido waje su na dubanta da son jin sauran bayani. Aminu yace,"Yagana me ya faru?, ba dai matsalar gas ɗin bace kumawa?". tace,"a'a wannan matsalar ai tafi ta gas...to Aminu kaga ina zaune ina kallon tashar saudiya sai ga Alhaji Amadu yazo kaina yay zandardar kamar sandar ba'are, fuskar nan a murtuke ya hauni da masifa kace Allah ya jiƙan rai Babana Manniru, wai dan me zan hana akai su waccan abar Shufin, na daina yi masa irin haka baya jin daɗi ko babu komai arziƙinta ake ci a gidan nan...wallahi saboda ban san zancen ba sai na riƙe baki ina d
🏠