Mairo ta mutu, Mairo ta mutu tun daƙiƙu kaɗan da suka shuɗe, yanzu Hussaina ce a gabanka".
har yanzu fuskarsa na nuna bayyananniyar ɗumbin damuwa yace,"Mairo bata mutu ba, da Mairo da Hussaina duk ɗaya ne". "a'a Baba ba ɗaya bane, Mairo da ubanta, ba shegiya bace. Hussaina kuwa bata da uba, ƴar gaba da fatiha ce, shegiya ce, sai da akayi zina sannan aka sameta". kowa yay shiru ya kasa cewa komai, illa sheƙar kukana da na Kulu ko kuma nace Akila ke tashi. na buɗe murfayen idanuwana sosai na kalleta, kallon da zan iya kiransa da na dole, domin ko kaɗan bana ƙaunar sakata a cikin iɗanuwana saboda na tsaneta. kuka ta ke sosai ba don ta tsoshe bakinta da ɗan kwali ba babu abin da zai hana sautinsa fita. na rufe ido na buɗe sannan na lashi leɓena na ƙasa, zuwa wannan lokacin kam idanuwana sun bushe, zuciyata ta ƙeƙashe, nayi gutun murmushi me cike da tarin ma'anoni da yawa sannan na buɗi baki na kira sunanta."Akila". yanayin yanda sautin muryata ta fito kaɗai ya isa ya shaida maka ba kiran kirki bane, sunanta kawai na kira, amma kamar har da Baba da Ya Kabiru na kira, domin duk idanuwansu suka sauke shi a kaina, sai ta ɗago da sauri ta dubeni, nace da ita,"ki nemi wuri ki zauna yanda za ki yi kukan da kyau, yanzu ba komai kike ba hawayenki ɗaya yake da dariya a wurina. ki bari in hukuncin abin da kika aikata ya biyo baya sai kiyi me dalili, dan wallahi tallahi Akila sai na ɗau fansar rayuwata akanki". Ya Kabiru ya ɗaga min murya da cewar,"ke kina hauka ne". maganarsa ta fito a dai-dai lokacin da ƴan gidanmu su ka fara sallamar shigowa ɗaya bayan ɗaya, ban dubi kowa ba, ban kuma bi ta kan kowa ba dan duk bata tasu nake ba. na buɗi baki zan kuma magana Ya Kabiru ya sake buga min tsawa,"karki ƙara cewa komai a wurin nan, ki wuce ki tafi ɗaki...". nima nai saurin dakatar da sauran maganarsa ta hanyar ɗaga masa hannu da cewar,"dakata Kabiru, magana ake ta rayuwata da kuma asalina, so don't interfere". sai kuma na juyo a fusace na fuskance shi ina nuna masa yatsa,"idan kuma kaƙi ji, to ina me tabbatar maka da hukuncin kisan da nake ƙoƙarinyi zai dawo kanka, dan a yanzu zuciyata na azalzalata ne na kasheta, idan har ita bata ji tausayina ba ta biyewa son zuciyarta ta aikata zina sannan ta haifeni, to nima ba zanji tausayinta ba dan na ɗauki kowanne irin makami na daɓa ma ta a ƙahoton zuciya ta shura". muryar Baba ta fita da kalmar,"innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Hasbunallahu wani'imal wakil". kalamai biyun da yake ta maimaitawa kenan a bakinsa, yayin da a gefe guda Inna Amarya da Inna Zulai ke aikin tambayar me ke faruwa. nasa hannu na ture Inna Amarya daga gabana na ƙarasa gaban Akila na tsaya, da yatsa ɗaya na ɗago fuskarta da ke duƙe tana kwaranyar hawaye. "wallah kin cuceni, kuma Allah ya isa tsakanina da ke, dan kin nakasta rayuwata, me nayi miki da har kika zaɓi ki haifeni ta wannan ƙazantacciyar hanyar?". na ƙarasa faɗa ina damƙar ƙirjinta,"wallahi tallahi ba zan taɓa yafe miki ba, sai na saka ki kuka fiye da wanda zanyi, sai na sakaki baƙinciki fiye da wanda kika saka ni a cikinsa, sai na zama ni ce ajalinki dan baƙin cikin abinda zan aiwatar ne zai sa zuciyarki ta kumbura ta fashe. a cikin daƙiƙa biyu da kunnuwana suka gama jin asalin labarin rayuwata daga gareki, a rabin daƙiƙa ƙwaƙwalwata ta gama lissafi da tsarin yanda zan ɗauki fansata akanki da Major, kuma a rabin minti zuciyarta ta zartar hukuncin kisa akanku, to amma cikin shigar sabuwar daƙiƙa lissafi da tsarin komai ya sauya, naga kasheku ba shi ne mafita ba, idan na kasheku ba shi ne zai sa na sami sauƙin zafi da raɗaɗin da ku ka dasa a zuciyata ba, ba shi zai hanani jin baƙin cikin rayuwata ba. in sakaku kuka fiye da yanda kuka sani shi ne kaɗai zai sa na sami ƴar salama daga ƙuncin da ku ka jefani aciki, a ƙalla ko ba komai za ku ƙarasa rayuwarku cikin dawwamammen baƙin ciki. Akila za ki ce na faɗa miki, ki aje hakan a ɓangaren tunaninki... wallahi ba za kiyi danasanin samar da ni ta hanyar fasiƙancin da ki kai ba sai na ɗauki mataki akanku tukunna, zan je na sami shi abokin dadiron naki, zan tabbatar masa da cewar ni ƴarsa ce da ya haifa a waje yay watsi da rayuwarta saboda yana so ya tsira da mutuncinsa, bayan yaji wannan zan tilasta masa na tursasa shi ya kwanta da ni ya aikata irin abin da ya aikata da ke, zai mu'amalantu da ni ne yana kuka yayin da nawa hawayen suke a ƙyafe. da zarar buƙatata ta biya zan wuce na nemi ɗan'una na shaida masa ni wace ɗinsa, na kamo hannunsa na kawo shi har gabanki, shi ma ya tursasaki ya aikata the same abin da muka aikata ni da major... kukan da zanga kina yi a wannan lokacin shi ne burina, duk da na san hakan ba shi zai wanke min dattin baƙin cikin da ke zuciyata ba, amma kuma ko banza na dasa muku baƙincikin da ba zai taɓa bari ku ji daɗin rayuwa ba...in Allah ya yarda ba za ku zubar da hawayen ruwa ba hawayen jini za ku yi ta zubarwa".
ta riƙe hannuna ta ɗauke daga kan ƙirjinta, dan ni kaina ina jiyo yanda ƙirjinta k