n fushi, kuma kaga su wadannan siffofine da basu da kyau, sam fushi bashi da kyau. A duk sanda mutum yayi fushi, idan ba anyi dace ba yana iya aikata abinda daga baya zezo yana dana saninsa shi yasa da wani mutum ya taba zuwa gurin Manzon Allah SAW yace yayi masa Nasiha se Annabi yace masa 'kada kayi fushi' ya maimaita masa hakan har sau uku.
Bayan haka akwai hanyoyi da dama da mutum zebi gurin ganin ya kare kansa daga fadawa dana sani dalilin fushin zuciya shine ta hanyar lazimtar ambaton Allah, a duk sanda kaji zuciya ta yunquro maka tana raya maka aikata abinda yake ba daidai ba kayi qoqari gurin kama Ambaton Allah, kayi hailala kayi Istigfari kayi tayi har se kaji wannan Fushin ya sauka.
Bayan haka abu na biyu shine yin shiru a duk sanda kake cikin Fushin, idan kasan bude bakinka a lokacin fushi baze sa ka furta a khairi ba to kayi shiru ka kama salati
Na uku shine nisantar duk abinda ze jawo motsuwar Fushinka, idan gurine kake zuwa ake bata maka rai to ka nisance shi, idan wani mutum ne ko wasu mutane suke tunzura ka zuwa ga fushin toh ka rabu dasu hakan shi yafi zama Alkhairi a gare ka, idan ma wani abu ne kake yi duk ka dena se kaga mutum ya zauna lafiya a rayuwar sa.
Ke kuma yata maganar kishi kiyi qoqari ki sassautawa kanki, mace ce ke wata rana gidan wani zakije ba kuma ki da tabbacin ke kadai zaki zauna dashi a rayuwarki. Baya ga haka a koda yaushe ki tuna cewar Allah ne ya halastawa maza damar ajiye mace sama da daya dan haka ba wani abu bane ba kuma abin da zesa ki daga hankalinki bane kama ta yayi ki ringa Addu'ar koda Allah ze kawo miki abokiyar zama ya baki wadda zaku zauna lafiya, amma wannan mugun kishin baze haife miki Da me ido ba dan bama ko wanne Namiji ne zeyi sha'awar auranki ba saboda gudun abinda ka iya faruwa a gaba".
"Saboda kalamsa basuyi mata bama sam hana kanta fahimtarsu tayi ta hanyar tafiya dogon tunanin, seda Abba ya kira sunanta da qarfi kafin tayi firgigit ta farka, malam ya hada mata yan magunguna na tsari da baki ya bata itama Mama aka bata wasu kafin sukayiwa Malam sallama suka kama hanya.
"Yanzu Alhaji meyw abinyi, tubda matsalar nan bata Iska bace inaga fa toh sedai asibiti ko abin a kwakwalwarta yake" Mama ta fada cikin Jimami, Umaimah dake bayan mota ta tunzura baki, daga iskoki kuma yanzu Tabin hankali ake yayibo mata? To ai shikenan aje duk inda za'aje kudinsu ne zeyi ciwo tunda dai ita tasan lafiyarta qalau.
"Gaskiya Hajiya Babu inda zan sake zuwa kuma, kindai ji abinda Malam ya fada ita zatawa kanta fada ruwanta ta sakawa zuciyarta salama ruwanta taci gaba da abi da takeyi mudai Allah ya gani iyayi munyi namu zagi kuma da take jawo mana ita ta sani" Abban ya fada a fusace maganar Malam ta babu me auranta tana dawo masa, kwarai gaskiya ya fada dan duk wanda yayi aure yayi ne dan ya samu cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali, waye ze siyi tashin hankali da kudinsa ya kai gida? Duk ma wanda yazo yaga halinta doke ya gudu ai su kansu dan babu ya da suka iya da ita ne sun kuma karbi hakan a matsayin tasu Jarabawar.
"Haba Alhaji ka dena fadar haka, gatan da zamu mata kenan a yanzu mu tabbatar da lafiyarta saboda nidai wadannan abubuwan da takeyi ban dauke su a mutum me cikakken hankali ba, kaga yanzu idan Asibiti suka tabbatar da lafiyar kwakwalwarta daga nan zamu san matakin da zamu dauka akan ta tu da munsan zallar iskanci ne abinda takeyi" Mama ta sake fada cikin kwantar da murya.
Yi yai kamar bazeje ba sedai meya tuna ya zaro wayarsa ya kira wata lamba, bayan sun gaisa a taqaice ya tambayi mutumin yana gida ne ko Asibiti kamin ya kashe ya mayar da ita Aljihu. A lokacin har sun kusa isa gida ya karkata kan mota suka qara gaba, a zaton Mama zasuje Asibitin Malam ne ko Murtala se gani tayi Abban ya dauki hanyar Dawanau.
"Alhaji Dawanau zamu je ne?" Ta fada tana kallonsa, se ya juyo a fusace yace
"Can zamuje Malika, ko akwai inda suke da kwararrun likitocin manya da qananan mahaukata ne banda can din? Ki fa rabu dani idan ba haka ba tam" ya buga sitiyari, shiru Mama tayi dan da alama ran maza ya baci, shi kansa zafin ran na Umaimah ai daga gurinsa ta gado kawai dai nata ya zarce nasa ne amma shima ai ba baya bane a yanzu ne da shekaru suka ja ya rage wa kansa hayanjya da fada saboda hawan jini ammada akan qanqanin abu be qi ya wuni yana fada da mita ba.
Tsuru Umaimah tayi a bayan mota, Dawanau fa yanzu haka zaa kaita a daura mata injinan da ake saka mahaukata karfa a garin neman gira a lalubo mata haukan da bata dashi. Kamar tace kar aje amma tasan yanda Abban ya hasala beqi ya tsaida mota ya lallasa ta suji gaba da tafiya ba, tana ji tana gani suka isa Asibitin da tundaha haraba ha kalinta ya fara tashi ganin masu lalurar rangwamen Hankali kala kala an fito dasu suna ta hidimominsu. Harta hango kanta ance zaa ajiyeta anan, ai bata san sanda ta ruqunqumo mama ta baya ba ta zabura tace
"Subhanallahi jikin ne Alhaji kaga ni ko daga zuwa abu ze kuma rikicewa". Tsabatmr takaici ko kallonsu Abban beba har ya qarasa yayi parking mo