a duba Amir din, Nasir ne ya bude mata qofa yace ta koma gaba, ba tayi niyya ba da taso ta mayar dashi Driver ne ya jata ya kaita gida amma ta daure ta sakko ta koma gaban.
Seda ya tsaya a wani guri ya siyo Youghort na L and Z manya guda uku masu Azabar sanyi da ruwan gora kafin suka ci gaba da tafiya. Youghort din ya miqa mata guda daya da ruwa ya ajiye ragowar
"Ban iya cin abinci a waje ba indai ba girkin Hajiyata ba sedai kona matata idan nayi aure shiyasa kullum wuni nake ina shan youghort idan bana gida" Khalil ya fada da son kawar da shirun da sukayi. Seta tabe baki, haka kawai ta samu kanta da cewa
"Amma ka iya zuwa Restaurant a Lagos kaci abinci har ka yi zance da yammata".
Kallon ta yayi cikin rashin fahimtar inda zancenta ya dosa yace
"Waya gaya miki naje Lagos?"
"Aljanuna ne suka gaya mun" ta bashi amsa kai tsaye, se ya saki murmushu, tana da tsiwa, kamar a jininta abin yaje hakan kuma kyau yake qara mata daidai sanda suka zo kwanar gidansu bisa kwatancen data bashi tace ya tsaya a nan.
"Har munzo ne?" Ya tambayeta yana gyara parking. Kayanta ta shiga tattarawa tana cewa
"Aa ka sauke ni a nan na qarasa cikin layi, bana so aga ka sauke ni a mota"
"Saboda me?"
"Saboda zaayi mun fada ace waye kai?" Ta bashi amsa a qage, dan bata so wani ya ganta, jiya jiya Mama ta gama yi mata fada akan shige shigen motocin samari kullum da wanda ze sauketa a gida da sunan abokanan aikinta hakanba mutunchi bane yanzu se mutane su chanza mata manufa dukda ita ba wani abu ta aikata ba.
"Mu qarasa, idan kina gudun fada ne zan shiga har cikin gidan na gayawa Mamanku ni na kawo ki bazata ce komai ba" Khalil ya fada yana taka motar ya shiga cikin layin,
"Se kace tasan ka, nidai ka koma baya ka sauke ni kawai dan Allah hakanma nagode" ta fada kamar zatayi kuka, be kulata ba yaci gaba da tafiya bata da zabi ganin yana neman wuce gidan ta tsayar dashi, a gurguje tayi masa sallama ta fice a motar, Layin kamar anyi shara babu kowa saboda uwar ranar data kwalle ta samu ta shige gida, ita kanta tana jin yanda gaba daya jikinta ya game da qamshin turarensa wanda ya kama motar.
Tsakar gidan ma babu kowa se Anty dake girki a kitchen ta rabe daga qofar gurin saboda rana.
"Allah shi qara, baku iyayi masu tausayin miji ba kuka jajibowa kanku girkin ice ai gashinan kuna ji a jikinku" Umaimah ta fada a zuciya, a fili kuwa murmushin qeta tayiwa Antyn harda gaisheta da yi mata sannu da gida ta wuce dakinsu saboda ta hango qofar Mama a rufe qila bata nan.
"Kai Yaya Umaimah turarenki dadi, zanzo dan Allah ki sammun, Salman qaninta ya fada daidai sanda tazo giftashi, tana qoqarin bashi amsa Mama ta shigo gidan da sallama idonta akan Umaimah data duburburce, Addu'arta Allah yasa Maman bata ga shigowarta ba.
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 6
Kallo daya Mama ta mata ta girgiza kai kawai ta shige ciki dan akan idonta Umaiman ta fito daga motar Khalil tana tsaye a soron gidan Maman Nana dan ta aiki Nanan tun tuni taji shiru ga babu yaron da zata tura shine tabi sahu da kanta. Ita dai fatanta kullum Allah ya shiryi Umaimah yasa ta ringa jin magana, bata zarginta da aikata wani abu amma wannan shegen rawar kan nata da kwashe kwashen ya isa ya janyo mata magana abinda batayi bama ace tayi.
Umaimah ko dakin su ta shige tunda dai batace komai ba idan ma ta gantan ai shikenan, ruwa ta fara watsawa saboda mugun zafin da ake ta saka doguwar riga me siririn hannu da hula ta nufi kitchen inda Anty take girki, yau Alhamis tasan dole a samu dan farfesun wani abun saboda kusan kowa na gidan yana azumi, litinin da Alhamis din kuwa se Abba ya siyo abinda zaayi romo aci da buda baki duk satin Allah.
Tundaga tsakar gidan kuwa ta fara jiyo qamshin dahuwar nama, ta hadiyi yawu tayi murmushi kafin ta qarasa daga qofar kitchen din ta kalli Anty da ido yayi ficifici saboda hayaqi ga zafin wuta gana gari tace
"Sannu Anty, an abinci ya sauka ne a sammin yunwa nake ji"
Murmushi Antyn ta mayar mata, harga Allah har cikin zuciyarta tana qaunar Umaimah amma a duk yaran gidan babu wanda ya rainata yake mata rashin kunya da diban Albarka irinta duk cikin taya mahaifiyarta kishi wadda ita sam ko a jikinta, tunda aka aurota bazata iya cewa yau ga ranar da Mama Malika tayi mata wani abu da sunan Kishi ba sedai sabani irin wanda kowanne yan Adam suke samu in dai an zauna amma kam maceceme tsananin kirki data kama girmanta haka tsayyaya ce aka yaranta kaf dinsu girmama Antyn suke hatta da Aminu da zasuyi Sa'anni idanya zo gidan yanda ze durqusa ya gaida Mahaifiyarsa haka ze durqusa mata wannan me ido atsakiyar kan ce se Addu'a kuma ita sam halin Umaiman ma ba damu ta yake ba.