a jiyota daga cikin gida ranta ya baci ba da wallahi seta masa rashin mutunchin da har ya mutu baze manta da ita ba.
Haka ta shige gida sukuku babu wanda yasan abi da ya faru tasha kukanta a daki washe gari tayi qaryar bata da lafiya dan haka bataje aiki ba.
Kiran gaggawa ta samu daga makaranta akan wasu takaddu basu cika ba na credentials dinta, dole ranar litinin ta debi original din duk wata takadda data san zaa buqata a makaranta ta tafi. Seda ta gama duk abinda zatayi a Academic Office har zata fice daga makarantar tace bari ta leqa Office din Sir Nasir su gaisa saboda anyi zaman mutunchi dashi.
Tun daga bakin qofa tutarensa yayi mata sallama, daga ciki take jiyo muryarsa yanayiwa Nasir din bayani akan abinda bata san ko meye ba. "Kinji Husky voice dinsa Umaimah" Kalaman Nabila suka dawo mata, lokaci daya taji ranta ya baci kamar ta juya se kuma ta tura qofar office din nan rai a hade kamar wadda ta kawo saqon mutuwa.
Nasir da Khalil suka juyo a tare suka zuba mata ido, Nasir ya saki murmushi yace "wata sabon gani, Hajiya Umaimah ce yau a office din mu bismillah shigo mana".
Qarasa shiga ciki tayi ba tareda ta kalle su ba tayi musu kudin goro ta gaishe su, haka kawai take jin haushin Khalil din da bema san abinda take ba se faman doka mata murmushi yakeyi.
"Yar unguwarmu kwana da yawa?" Khalil ya fada yana kallonta, kamar kuwa tana jira ta doka masa uwar Harara harda murguda baki, gani take kamar ma suna tare da Nabilan, qila ma soyya tayi nisa har suna shirin aure.
Jan ta Nasir ya ringayi da hira amma ina hankalinta na kan Khalil daya duqar dakai yana dannan waya yana murmushi, Albishir ne akayi masa, ya samu aiki da wani babban construction company a Lagos interview din yaje kwanaki har Nabila ta ganshi tareda wani abokinsa Taufeeq Babatunde wanda shi yayi masa hanyar aikin da yake Babansa babban mutum ne a Lagos din.
Yanzu yana gaya masa ne cewar comapany sun bude branch a nan Kano dan haka anan ze zauna.
Ita kuwa Umaimah gani takeyi ai da Yammata yake chatting zuciya tayo sama fuu ta fizgi jakarta murya a cunkushe tayiwa Sir Nasir sallama ta fice yana tsayar da ita amma taqi tsayawa.
Dagowa Khalil yayi jin an buga qofa da qarfi yace "lafiya? Me aka mata?"
"Kai zan tambaya dan tunda ta shigo kai naga tana harara da alama ka mata wani abun ne" Nasir ya fada yana dariya.
"Ni a ina zan ganta na wanta wani abu?" Ya fada yana daga hannu sama, Nasir daya miqe ya fara tattara takaddu yace
"Na sanin muku ba naji kace yar unguwarku ba waya sani ko tuni kun jone babu labari"
"Can da dadewa ne naganta a gidan mu an aiketa kai naman suna, ashe sister matar Habib Neighbor din mu ce, shine muka gaisa daga nan sau daya na sake ganinta tare da wadannan qawayen nata masu kalar rashin ji kusan six months kenan fa se yau na sake ganin ta ma ni" Khalil din ya fada cikin son kare kanshi.
"Nifa bance wani abu ba kake koro mun bayani kamar wani Lawyer, muje dan Allah ka sauke ni gareji na dauki motata nasan yanzu an gama gyaran, qarfe hudu zan kai Amir dressing Asibiti" Nasir ya fada bayan daya dauki abubuwan da ze buqata ya nufi qofa. Miqewa Khalil yayi shima yabi bayan sa yana cewa
"Dressing name? Meya samu Amir din?"
"Wallahi qonewa yayi da ruwan tea a qafa amma da sauqi inagadaga yau ma mun gama zuwa" Nasir ya bashi amsa daidai sanda suka isa gaban Motar Khalil din daya siya kwanannan Toyota Yaris Fara me kyau da ita.
Suna tafe yana masa qorafin rashin gaya masa qonewar Amir din suka isa get, rana ta take dan haka ana wahalar abin hawa.
Daga can gefe suka hango Umaimah a rabe fuskar nan kamar hadiri kai kace zata fasa kuka da alama tasha tsayuwa har ta gaji dan a jingine take da bango.
"Ga mutuniyarka can fa inaga ta rasa ride ne" Khalil ya fada yana kallo ta, se Nasir ya waiwaya shima ya kalleta yace
"Kai dai duk inda yarinyar nan take se idon ka ya hasko maka ita, toh ka mata lift ka kaita gida mana tunda hanyar ku daya"
"Bafa hanyar mu daya ba na gaya maka gidan sister tane a layin mu kai ka fiya matsala wallahi"
"Toh kaga daga nan seka gano Asalin gidan su mana ko ni me nace ne" Nasir ya fada yana qunshe dariya. Qarasawa kusa da inda take ya danna mata horn. Hararar da tayiwa motar idan da ace mutum tayiwa se ya kusa faduwa qila, ta qara tunzura baki gaba, ita ba akan titi take ba bare ace ta tare hanya amma koma waye ya kuskura ya qara mata horn seya gane kurensa.
Nasir ne ya sauje glass din bangarensa ya kalleta da murmushi yace "kina tsaye a rana abin hawa yayi wahala koh? Bismillah muje mu rage miki hanya".
Badan gajiya da ranar da ake kwallawa ba da babu abinda ze sa ta hau motar mutumin nan, tana qunquni haka ta bude baya ta shiga, sanyin Ac da qamshin turarensa suka sakata sakin ajiyar zuciyar dole seta qara bajewa tana jan iska a hankali, ta centre mirrow yake kallo ta ta sani amma tayi kamar bata san yanayi ba a ranta cewa take " shi kuma ciwon kallon mata ne dashi qilan.
A hanya Nasir ya sauka suka rabu akan da daddare Khalil zeje gida y