uka hadu da wanda yake zaune akan Kujerar gefen, kallo daya ta masa ta dauke kai dan vata taba ganin fuskarsa a office dinba is dai idan sabon ma'aikaci ne aka dauka suka qarasa gaban teburin suka gaishe shi ragowan suka waiwaya suka gaida baqon banda Umaimah data kafa kai tana binciko musu Exam cards dinsu a jikinta tana jin ido na yawo akan ta abinda yasa ta ringa sakin gajerun tsaki kenan tana mita a ranta.
Ita ta ringa miqa wa kowa nata suna signing a takaddar dake gefe har suka gama, dake ita ce qarshen fita seda takai bakin qofa kafin ta kalli baqon dake binta da kallo tunda suka shiga ya kasa dauke idonsa akan ta ta maka masa harara qasa qasa tace
"Ayita kallon mutum kamar an bashi ajiya saboda sa ido" tayi waje abinta.
Tsaf ya ji abinda ta fada se kawai yayi murmushi ya kalli abokinsa dake cewa
"Umaimah kenan, sarqa uwar rikici. In kana neman danger wutar baya ka samu yarinyar nan ka gama kawai abokina"
"Allah ko? Ni kuma ta burgeni. Da ace na shirya aure dana gwada sa'a ta dan a kallo daya ta shiga raina kuma tayi dai dai da matar da nake so na aura".
Hannu ya bashi suka tafa yana cewa " Bayero Bayero namu, to ka afka mana, amma fa karka ce ban gaya maka ba zaka sha rikici da ciwon kai a gurin nan kai kuma gaka ba gwanin daukar hayaniya ba"
Murmushi Khalil yayi yace "toh ai hadin shine daidai, idanna dakko mara hayaniya irina ai gidan mu will be boring, gara dai a samu wadda zata ringa mayar dashi lively"
"Hakane, toh Allah ya tabbatar mana da Alkhairi abokina, kace wannan ziyarar bazata da ka kawomun ashe rabone ya kiraka"
"Amin amma da saura, ni yanzu babu ma shirin aure a gabana kasan dai yanda ake lallaba rayuwar ga aiki yaqi samuwa yar buga buga kawai akeyi, qoqari nake na gama hada Masters din nan nayi settling. Akwai abubuwa da yawa danake da buqatar kammalawa kafin na dakkowa kaina maganar aure tunda bazaka dakko yarinyar mutane kazo kana bata wahala ba dole tana da buqatar abubuwan more rayuwa ko yayane a gidan ka" Khalil ya fada.
"Hakane, amma kuma ko a yanzu Bayero ai Alhamdulillah rayuwarka na tafiya daidai zaka iya ajiye iyali, mutum nawa kafin cikin abokan mu da suke aikin abin fa duk intihani ne kawai amma idan kace seka samu yanda kake so zakayi aure zaa dade gaskiya" Nasir ya fada.
Se Khalil ya gyara zaman sa yace
"Hakane nima ba wai ina nufin sena tara kudi zanyi aure ba komai rabo ne a rayuwa, ta yuwu ma naka arziqin seka yi auran zaka same shi amma yanzu Nasir kadai san nauyin gidan mu a kaina yake. Nine ci, sha da suturar mahaifiyata da qannena guda biyu da suke gabanta, kai har masu auran idan suna da wata buqata nifa suke kira ka sani.
Yanzu haka ni ina Masters, ga Jalila nk nake dauke da nauyin karatunta, Halifa bana ze gama secondary ya shiga Jami'a shima ga dai abubuwa nan kala kala babu yanda zaayi yanzu na tattago maganar aure da wadannan nauyin a kaina bayan ba wani kwakwkwaran aiki ne dani ba, bani da muhallin da zan ajiye mace a yanzu, samun nawa na lokacine, se mun samu yar kwangila anyi sannan muke samu, muna dai ta fatan Allah ya buda ya bamu yanda zamuyi tunda dai Allah yaga zuciyar mu".
Numfashi Nasir ya sauke yana kallon abokin nasa da tausayawa, rayuwa kenan. A shekarun baya idan akace akwai wata rana da Khalil Bayero zasu shiga halin da suke ciki a yanzu babu me yarda. Irin gatan da suka tashi a ciki, mahaifinsu tsayayyan mutum me wadata iyalansa su kansu sun shaida tarin Alkahiran sa a rayuwa dan da yawan abokan Khalil da sukayi primary tare ta gomnati lokacin da budi yazowa babansu ya chanza musu makaranta zuwa ta kudi haka ya hada dasu duka ya kaisu ya ringa biya musu kudin makaranta.
Banda Scholarship daya samar musu na fita qasashen waje sukayi karatun degree dinsu gashi yanzu ganiyar sa suke ci, duk kuma abinda suka zama a rayuwa sanadin sa ne.
Bayan rasuwarsa ne abubuwa suka damewa iyalansa, wani amininsa da suke harkar kasuwanci yazo da takaddun da duk me hankalin daya gani yasan na bogi ne akan yana binsa bashin wasu maqudan miliyoyin kudade, ya samu goyon bayan qaninsa da suke uwa daya uba daya wanda ya bada shedar zur a kotu kan Marigayin da bakinsa ya gaya masa cewar akwai bashi tsakaninsa da Alhajin amma kuma babu wanda yasan da hakan ciki harda matarsa da Kuma Khalil din kansa wanda a sannan kusan komai na Mahaifinsu shine akai.
Ansha badaqala musamman da Iyalansa suka kafe akan basu yarda ba, da ace akwai irin wannan magana me muhimmanci da Alhajin ya fada tun yana jinya tunda ba mutuwar fuji'a yayi ba yasha jinya sosai da har seda ya fitar da rai da rayuwa kuma a sannan seda ya fadi duk wani da yake bi bashi ko shi ake binsa amma da yake duniya babu gaskiya, aka je kotun ma suka siye Alqali suna ji suna gani haka suka tattara kudaden daya ce suka bashi wanda seda suka hada da siyar da kadarorinsu kafin suka tada kudin, qarshe gidan da suke ciki kadai suka tsira dashi se wani qarami da suka saka yan haya a ciki. Duniya kenan wata shari'ar se a lahira.
Hira suka taba sosai kafin Khalil yayi masa