unnen general".
Ta fada suna nufar kofar fita daga falon.
"Da dai kin yiwa kanki gata"
Yaya Ishaq ya fada.
*********
Tun safe su Mahmud suka fita da Sameer su shiga can su fita can duk da Sameer Kusan Dan kallo ne an Kai ruwa Rana kafin a samu ganawa da Wanda alhakin matsalar ke hannunsa Basu suka dawo ba sai dare a gajiye suka dawo Jin dadinsu daya ba a hotel suka sauka ba gida ne. Sameer yayii musu order din abincin Africa. Saida sukayi wanka sannan sukaci abincin inda Allah ya taimaka sunyi sallah a wani masallaci a hanya. Bayan Mahmud ya shiga daki wayarsa ya Ciro ya shiga ciki gurin da akayi Masa connecting da CCTV nan ya lalace gurin kallon Zahra yanda yake more kallonta yasan da ace tasan da CCTV a dakin bazata Bata sakewa haka ba tana sabgoginta. Amma ganin ita kadai a dakin take zuba yanda takeso, amma yanda ya fuskanceta kamar wani Abu Yana damunta ya Raina yanda take walwalarta, ya rasa aikin me suke ita da Mai Taya ta zama Dan gani yayi ita Mai tayata zaman ta fita waje da alama wani Abu ta sawo Dan can baya yaga ta hada wuta da gawayi akan wani Abu ta Dora tukunya Mai Dan girma, so yake yaga wace wainar zasu toya.
Dayar wayar ya dauko Yana kokarin kiranta sai kuma Kiran Mr Lee ya shigo akan Yana fada Masa kome yake ya fito bakin da zasuzo daga Thailand sun karaso shi kadai ake jira, tashi yayi Yana Kiran Sameer akan ya zama ready zasu fita.
**
ZAHRA.
Tun bayan data gama break Basu zauna ba aiki Zahra ta dauko dambun Nama take son yi yau akwai Naman da yawa sai kuma abinci shima Mai Dan yawa haka Nan taji tana son kaiwa Abban ta da Baba Malam abincin juma'a zilai ce tace a sawo kufat ayi suyar dambun a Kai tunda da yawa za'ayi ta Bata kudin aka sawo ta Dora, Basu suka Gama aikn ba sai bayan azzahar zilai ita ta mikawa zayyan bayan ta wuce ne ya bude abincin yaga irin garar da aka kawo Masa yayi ta mamakin yanda matar oga ta iya girkin hausa haka Mai shegen Dadi gashi ita Kuma ba bahaushiya bace ko Ina ya samo wannan da Kuma dalilinsa na zabar wannan rayuwar shifa ko a mafarki baiyi tunanin ogan nasa ze iya sakewa har ya Mike kafa yayi zamansa a irin wannan muhallin ba da iyalinsa, haka yayi ta sakawa Yana kwancewa.
Sai da su Zahra suka Gama Zuba komai a mazuban da suka Dace sannan Zahra ta wuce ta Kira magaji a waya akan yazo tana nemansa sannan ta shige wanka sai bayan la'asar magajin yazo lokacin ita kadaice a falon tana tulawar alqur'ani, Saida ya cika cikinsa Yana zuba Santi sannan ta bashi yace ta fito Masa na Baba Malam Dana gurinsu Ammah har ya Kai kofar fita daga parlour ya juyo Yana fadin "inyeeh su Adda Zahra an girma har an Fara aikin neman ladar tsaffi da fatan dai kin fadawa mijin naki kada garin neman lada a kwaso zunubi". Ya karasa fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka magaji Kai Kullum baka girma ko?"
"A'a zancen gaskiya ne Dan bawan Allahn nan baki San yanda yayi ya Nemo kudin sayen kayan nan ba Amma kin tashi kin zuba irin wannan garar Dan kawai Kinga baya gari ko?"
Harararsa tayi "To nayi kayan nan dai nawa ne mijina ya aje min Bai Kuma yi min iyaka ba duk abinda nakeso zanyi dasu idan bazaka Kai ba dawo ka aje min sai Aunty zilai ta Kai ko naje da kaina". Ta taso ta nufo inda yake da sauri yayi gaba Yana fadin.
"Allah ya huci zuciyar uwar gidan Mahmud tuba nake".
"Dan rainin hankali shi dai gurinsa ya saka mutane magana".
Aunty zilai ce ta Bata amsa Sam Bata lura da fitowarta ba.
"Kema uwar dakina Kamar kin manta halin Mai sunan Alhaji ai shi burinsa Ke nan yayi jan magana".
"Ai sai yayi tayi tunda halinsa ne"
Abincin zilai ta kawowa Zahra Nan cikin parlour some times Bata fiye son zaman dining ba, kitchen zilai tayi niyyar komawa Zahra ta Hana "ki zauna a nan muyi lunch din Ina Zaki kuma koni bafulatana bana irin wannan d'abi'ar".
Sun Fara cin abincin kenan door bell din tayi k'ara zilai ce ta tashi taje ta bude Mujiba ce tare da wata yarinya Sa'ada 'yar makotansu.
"Kai! Kai!! Kai!!! Tab amma dai batan hanya kikayi Mujiba, yanzu Alkawari da amana sunce haka? Yaushe rabonki da gidan Nan?"
Dariya mujibar tayi tana fadar "eh lallai da sauranki irin wannan Baki zai- zai, Kuma shike Nan daga kawoki saina dunga sunturi a gidanki ai Mai gidan saiya saka Mai gadi ya hanani shigowa tinda Zan zamar masa matsala, Wai ke tsaya waye a gate din gidan nan daya tsaremu da dogon turancin daga Ina zuwa Ina me mukazoyi ke tambayoyi dai gasu nan kamar zanga Mrs president".
Ta fada Tana Zama a kujerar dake kusa da zahrar Sa'ada ma ta zauna.
Spoon din hannunta Zahra ta aje "Bari kawai Muji wlh Nima haka na ganshi haka Nan Rana tsaka ya canzawa Mai gadin gurin aiki ya mayar dashi makarantar gidan Baba Malam ya ringa share share ya kirawo wannan bansan ko daga Ina ba yanda aka wayi gari da Mahmud shima haka aka ganshi nifa lamarin yafi karfin tunani na kawai na saka ido ne Naga karshen film din".
Ta fada tana Dan tab'e Baki.
"Amman wlh Baki da kirki auren naki kike cewa film dan bawan Allah ya biya sadaki ya daukoki daga gidan ku ya killace ki gur