ensa na yawo cikin bakinta ya lalubo nata harshen cikin gentle yake tafiyar da ita ba kamar ranar nan ba, sun dauko Kusan minti biyar Yana Abu daya ji tayi kafafunta na neman gagarar daukar ta, jin jikinta na rawa yasa ya Kara mannata da jikinsa wani Nishi tayi ba Halin magana, kokarin yanye harshenta take daga Bakinsa Kai ya girgaiza Mata sai da yayi mai isarsa ya saurara Mata Kan gadonsa ta zube da gaske ya kashe Mata jiki ji take idan ta taka kafarta faduwa zatayi.
Dan rankwafawa yayi saitin fuskar ta "Haba 'yan Mata be strong Mana me akayi da maza inji karya, taso muje ki rakani idan na biye Miki labarin salo ze canza".
Ya kamo hannunta ya mikar da ita, jakar laptop dinsa kawai taga ya dauka, gyalenta wanda yake yashe a kasa ya tsuguna ya dauko Mata Yana rufa Mata a kanta.
"Zaki bani Aron motar ki naje Kano da ita? amma fa saina dawo na dawo Miki da ita a airport Zan bada ajiyarta yanda idan muka dawo saina karba kawai".
Kai ta gyada Masa alamar Eh.
*A'a magana zakiyi idan kin amince to idan Baki amince ba na nemi hanyar Tasha kawai".
"Ka dauka kaje da itan koka dawo ma na bar maka za'a kawo min wata ba kaji Abba ya fada ba".
"Ke! Kinsan kudin ta kuwa zakice kin barmin Dan ki hau Abba ya saya Miki, Aron ma Ina laifi".
Yaja hannun ta suka nufi kofar a falo ya tsaya Yana wasu 'yan dube duben da Batasan Kona menene ba sannan suka nufi harabar gidan, kasa hakuri tayi ta jefa Masa tambayar.
"Wai haka zaka tafi ba kayan sakawa da takalma da sauran abun bukatu ne?" Dan shafa gefen fuskar sa yayi ya Dan furzar da iska daga Bakinsa. "Bana tafiya da Kaya ai wahala ce nasan duk inda zani akwai na sayarwa na saya kawai, aikin gane?"kallonsa kawai batace Masa komai ba.
Saida yaje gurin Mai gadi ya bashi wata envelope sukayi maganganu sannan ya dawo gurin da take tsaye.
"Zan tafi sai Allah ya dawo Dani, ki kula da kanki bana son yawo Amma idan gidan Ammah ne ko Aunty Hasana idan Bata koma Jos ba kina iya Zuwa".
"To na gode, Allah ya tsare hanya ya bada sa'ar abinda akaje nema".
"Allahumma Amin. Allah ya tsare min ke daga sharrin mutum da Aljani da dukkan abinda yake cutarwa, ya Ubangiji na bar maka amanar iyalina ka Zama gatan mu".
Ya fada yana nufar motar, a hankali ta biyo shi ya bude ze shiga ta riko hannunsa ta Manna masa kiss a tsakiyar hannun. "Safe journey" ta fada da wata murya Mai rauni da gudu ta juya idonta fal hawaye. Tsaye yayi Yana kallon ta har ta shige ciki, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya shiga ya tada motar jikin window ta tsaya har Saida ya fice daga gidan.
________________________
Tunda Mahmud ya bar cikin gari ya saki motar, rabon da yayi tuqi irin wannan har ya manta, kyakykyawar awa daya da minti arba'in da Tara ta kawo shi Kano, daga Hotoro NNPC sai ya shiga ta ring road ya fita 'yan kaba haka ya dunga yayyankewa har Zuwa round about na sani Baban kwari Sannan ya nufi Malam Aminu Kano international airport,Yana daf da shiga gate din ya saka face mask da glass sannan ya shiga, wayar Sameer ya Kira tana daf da katsewa ya daga.
"Kana Ina? Na shigo yanzu ina fatan komai ya dai-daita?". Dan Jim ya yi yana sauraren sa. "Ok kazo ina parking lot inda ake bada ajiyar motoci".
Ya sauke wayar Yana kalon masu Kai da kawowa.
Yana Nan tsaye har sameer din ya karaso ya gaishe da Mahmud cikin girmamawa, jakar laptop din Sameer ya karba da key din motar ya nufi inda suke da alhakin karbar ajiyar, shi Kuma Mahmud ya nufi reception din.
Sameer Bai jima ba ya dawo da takarda shedar bada ajiya, sun Dan tattauna kafin lokacin tashinsu yayi, zasu shiga screening ne Mahmud ya Kira wayar zahra, tana kwance a gado rungume da pillow bayan tayi kukanta Mai isarta ta lallashi kanta tunda Babu Mai lallashin gani takeyi shima kamar ya tafi kenan. Ringing din waya taji da sauri ta tashi Dan ita Sam tama manta da wata waya tunda ya Bata Bata karabi takanta ba, da sauri ta dauko tana duba waye ya Kira MM DANGE ta gani wani sanyi taji ya saukar mata,
Picking tayi tare da sallama, sai kuma tayi shiru.
"Zamu tafi ne nace bari na kira na fada Miki, ko zamu sake waya ze iya kaiwa jibi kada hankalinki ya tashi idan komai ya dai-daita Zan kiraki in Sha Allah".
"Tom Allah ya saukeku lfy".
"Allahumma Amin my precious, please take care bye".
Ya katse Kiran yasan idan yaci gaba kuka zata saka Masa ya rasa wane irin idanu gareta masu saurin kuka.
Sha biyu da rabi jirginsu na kamfanin air Max ya daga.
Wayar tabi da kallo kafin ta aje kusa da ita, sai Kuma ta tashi kamar wadda aka zabura. Wayar ta dauko dubawa tayi wata baguwar number ta gani batayi kasa a gwiwa ba tabi Kiran Dan missed call ne tunna jiya. Cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga Bata jima Tana ringing ba aka daga muryar matashiyar macece daga ji tana ji da ajinta sallama Zahra tayi Mata suka gaisa sannan zahrar tace Mata taga missed call dinta ne a wayar ta.
"Missed call Dina gaskiya bani na Kira ba Amma Dan Allah wacece ke?.
Yar dariya Zahra tayi kafin tace "sunana Fatima Zahra Muhd sani Ni mazauniyar Azare ce ta jihar Bauchi".
Kit ta