in zuwa ne babu zani.
Tafiya yake da hanzari Dan ma safiya ce sosai titin ba yawan jama'a cikin Kan kanin lokaci suka shigo unguwar, Horn ya danna da karfi da gudu Mai gadin yazo ya bude yana fadin "barka da zuwa!"
Da gudu ya Koma ya dauko sakon dasu mama suka kawo jiya Yana fadin "barka da Asuba yallabai gashi jiya bayan futarku su Hajiya Babba sukazo suka bada a ajewa Hajiya".
Ya fad'a Yana risinawa Yana mikawa Mahmud ledar.
Saida ya karewa shi da ledar kallo, sannan ya hade gabas da yamma yace ka rika idan kana so, Kuma
Ka hade kayanka in anjima kadan binyaminu ze zo da Wanda ze canjeka aikin Nan adalci daya nayi maka ban koreka ba zaka koma share-sharen makarantar Yara kawai".
Jiki na tsuma Mai gadi ya durgusa Yana fadin "Yallabai me nayi haka da zafi Dan Allah kayi hakuri wlh baza'a qara ba ka rufa min asiri".
"Iya Alfarmar kenan bana korar ma'aikaci sai lefinsa ya Kai uku to Kai daya kayi ba tare da kasan laifi bane shi yasa nayi maka uzuri bazan rabaka da rufin asirinka ba dauki kaje yanzu Zan fito". Jiki ba kwari ya dauki ledar ya juya Yana ta faman tunanin ta ina ya kuskuro yallabai jiya lafiya kalau suka rabu yau Kuma ya tashi da canjin gurin aiki da Allah ma ya dube shi da Rahama daba Kora bace days shiga uku.
Suna shiga Mahmud yayi bed room dinsa ita Kuma ta nufi kitchen ta Fara hada abu marar wahala coffee ta dafa Masa sai sandwich kawai tayi shaf-shaf a tray ta Dora direct bedroom dinsa ta nufa ya fito daga wanka Yana goge jikinsa a ranta tace shi baya mura any time wanka kamar dangin kwadi.
Sallamar ta ya amsa Yana aje towel din dake hannunsa.
"Ke! Me kikayi daga zuwan mu ba dai abinci bane ko? Ni bana cin komai a irin wannan lokacin".
Langabe Kai tayi tana dubansa kasa-kasa har Zuwa lokacin wani nauyinsa takeji. Yana ankare da ita.
"Coffee ne fa da sandwich nayi maka Dan Allah kada ka tafi da yunwa,alhalin gani a tare da Kai ai da naji kunya daga zuwa ka nemi abinci a kanon".
"Inye ashe dai ana son mamudan?".
Ya fada yana nufar inda ya aje kayan da ze saka kananun Kaya ne na kamfanin Armani ya saka bako kunya ya cire rigar wankan ya tsaya daga shi sai boxer short, da sauri ta runtse idonta Dan Bata zata zeyi irin wannan abunba Yana kallonta ya basar yaci gaba da shiryawarsa, Zama yayi Kan sofa Yana umartarta ta kawo masa coffee din nan duka ta dauko ta aje gefensa ya dauka Yana sipping Yana kallonta tana Wasa da gefen veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya watsa mata kasa a ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin.
"Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota "Kinga gurin zamanki Nan ya dorata inda ya Saba..
"Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa kona dawo ko ba na dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan Nan ni dangatan iyayena ne da kakata Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na fadawa labarinki sai kakata ta sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira ya zauna yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na, Dan Allah kiyi min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena da Kima da daraja, idan Allah yasa na dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada min ba,
duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma nabar komai a Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje mata su a akan cinyar ta.
Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai dai hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki yaki kwanciya da ita"
"Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka tafi bazaka dawon ba".
Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin ajiye Mana babies a ciki idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin ki nema zani ki min addu'ar samun nasara".
✨✨✨
✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
Strory
&
Written
By
Maman Fateemah
Page 29
📖🖋️
_____ Sun jima a haka Yana lallashinta kafin ya dagota su tashi tsaye tare " me za'a bani nayi guzuri dashi?"
Ya tambaye ta, shiru tayi kafin ta Dan watsa hannu tana Dan kallonsa ta gefen ido.
"Ai kaga bamu kwana a gidan ba bare nayi maka wani Abu Saida idan biscuits din Nan Zan dauko maka sai ka tafi dasu na bada a sawo min wani".
Dariya abin ya bashi ita bilhaqqi da gaske take fada Wai biscuits kamar wani yaro.
"A'a niba shi nake so ba tsarabar da zan rike Ina tunawa da ita har na dawo".
"Me Kenan?" Ta tambaye shi cikin nuna rashin sani.
Jikinta ya matso sosai ya riko ta Yana kallonta da wani yanayi mai wuyar fassarawa, Bakinsa ya Kai Kan nata Dan bakin yasa Hannun ya talkafo kanta batayi zato ba tsammani taji harsh