cheque din Yana fadin.
"Ka rike a gurinka kawai a sawo kayan shagon Nan dasu a Fara kasuwar tunda Allah ya kawo kawai".
"A'a baza'a yi haka ba ka tafi dasu kayi guzurin Kamar yanda yace idan Allah yasa kun dawo sai asan yanda za'ayin".
"Kayi yanda nace ba wata damuwa acan komai Yi Mana za'ayi to me zanyi dasu? ga Kuma abun bukata a gida ba gara ayi ba watakila kafin mu dawo ka koma sari na biyu".
Ya fada Yana murmushi.
Majalissar su sukaje Mahmud yayi musu sallama har salisu Yana zolayarsa akan barin Zahra da zeyi Yana tsakiyar angwancewa. Bai Dade ba ya tafi duk hanlalinsa Yana kanta yasan har ta gaji da jiransa watakila ma tayi barci.
Saida ya biya ya saya musu kaza da apple ya dauki hanya.
Lokacin Sha daya da minti ashirin da bakwai.
A hankali ya bude dakin abin mamaki Zahrar ya gani gurin fridge da glass cup a Hannunta tana Shan wani abu, Sam bataji bude kofar ba saboda tv a kunne take sannan ta bawa kofar baya, Jin kamshin turarensa yasa tayi saurin juyowa lokacin yazo daf da bayanta, juyowar da tayi sai a cikin kirjinsa.
Ledar ya saki qasa yayi Mata kyakykyawan masauki ya saka hannunsa ya talkafo bayan ta, yasa Bakinsa a dai-dai kunnanta.
"Na dauka kin wuce Kano a barcinki Ashe dai jaruma na aura wadda take iya jiran mijinta komai dare". Ya karasa fada Yana Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunnen.
"Dan Allah ka Bari".
Ta fada tana niyyar janye jikinta shi Kuma ya Hana hakan. Dan kwabe fuska tayi, "ka sakeni toilet zani".
"Ba wani toilet idan Kuma da gaske ne muje na rakaki".
Kai ta gigiza, shafa gefen ribs dinta yayi yaji yanda rigar ta matseta komai yayi tsan-tsan. Dan sakinta yayi Yana Kare mata kallo daga sama har kasa, Dan sunan dinkin a tsokano fitina kawai, shi a dazu ai be karewa dinkin kallo ba sai yanzu a kausashe ya jefa Mata tambayar.
"Waye telan da yake Miki dinki".
Hannu yasa ba zato ya shafo gaban rigar da sauri ta saka duka hannuwanta ta tsuguna sai Kuma kasan ya baje. "Ya Salam" ya fada a hankali.
"Kinyi shiru Ina tambayarki".
"Makociyar Aunty Hasana ce take Mana dinki".
Ajiyar zuciya yayi yayi zaton namiji ne yaji ance sune ke gwada Mata idan hakan ta kasance ai an gama dashi wani ya taba Masa wannan jikin. Tsugunawa yayi ya kamota ya dago jikinsa ya maidata "ki barni naji duminki gobe ya wannan bana kusa dake Ina can na rungumi pillow, so muje muyi hirar yaushe gamo, ko Kuma ban sani ba murna kike kina Jin dadin Zan tafi na Baki space ki sake ko?"
Ya fada Yana Wasa da Dan Karamin zoben dake 'yar karamar yatsarta.
"Oya talk kinyi shiru koba haka bane daman ba kince min me naci Kamar maye na tsotseki waya sani ko maye ne ni ko Baki fada ba? Kawai Dan na koyawa bakinki ladabin magana da miji akan wannan yaron shine na samu lambar maita daga gurinki".
Sexy eyes dinta ta zaro Masa, abinda yake burgeshi yake matukar so kenan yaga ta tsorata.
"Ni nace maka maye? Yaushe akayi hakan Wana fadawa?"
"Abar maganar kawai sai ranar Dana cinyeki danya Zaki gane Ni maye ne".
"Wlh Ni ban fada ba, Toni Wana na gani da Zan Fadi haka har a Gaya maka, a kwanakin Nan ko waya ban rike ba fa".
"Naji shike Nan zo muje Naga aikin Allah yasa dai yayi kada aiki ya Koma baya"
Ledar tsarabarsa ya dauka ya jata suka nufi ciki. Gefen gadon ya zauna Yana janyo laptop din gefensa Zahrar na tsaye a dayan gefen.
"Hayo ta Nan ki bude ki nuna min aikin in gani". Ba musu tayi yanda yace Kan cinyarta ya Dora laptop din ya Dan kwanto jikinta yana ganin aikin har ta Gama nuna Masa, tab'a hannu yayi Yana fadin "inye kice idan Allah ya hure mun na samu sakatariya ta a gida basai na nema a waje ba, yanzu jeki saman fridge akwai plate biyu ki dauko kizo ki Zuba wannan" ya nuna Mata ledar daya shigo da ita.
Laptop din ta aje kusa dashi ta janyo gyalen da ta yafo zata yafa ya karbe Yana Mata wani kallo.
"Me zakiyi da shi ko akwai Wanda ba muharraminki ba a Nan da Zaki Kama rufe jiki, ok da bana Nan kin aje har Dan kwalin kina watayawa yanzu Kuma na dawo Zaki wani saka gyale tunda idan na ganki kin dauki zunubi ko?"
Shiru tayi Masa tasan idan ta magantu sai ta Kara laifi, juyawa tayi ta nufi kofa ya bita da idon Yana kistima abubuwa da yawa a zuciyarsa.
Plates din ta dauko ta kawo ta koma ta dauko ruwa roba daya da fresh milk tunda taga Kamar yafi son Shanta akan lemo.
"Dauki ki zuba" Nan ma ba musu ta bude kedar Naman wani kanshi ne ya doki hancinta har lokacin Kuma da zafinta, daya ledar ta bude apple din ta Zuba a kai, gyara zama yayi Yana nuna Mata gefen shi, Kaita girgaiza.
" Na koshi bana Jin yunwa".
"Naji ai ba abinci bane kizo kici ko nayi Miki dura da gaske nakeyi fa".
Narai narai tayi da ido, Allah bana cin Abu Mai yaji ko maiko da yawa da dare ulcer yake tada min".
Ture plate din yayi gefe ya janyota ya zaunar da ita a cinyarsa.
"Me Kika ce? Ulcer as how Kika kamu da ulcer, since when?"
"Bafa wani Abu bane tun Ina secondary ne Amma tunda aka fada min na rage cin wadannan abubuwan more especially da dare idan Zan kwanta saina daina ciwon cikin".
Plate din ya ture gefe, "tashi ki K