a yi Masa suka fice daga gidan.
Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan saida suka hada turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan kanshi da mazubai Wanda dole yayi attracting mutum.
Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai tambarin gurin Saida turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin gate din ya leko ya gane Mama tunda ya jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku".
Ta rusuna ya gaishe su.
'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa.
"Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau"
Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa suka fita da Mai gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku shigo su Kuma sun fita".
Turus sukayi wannan ta kalli wannan.
"Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin rain a maganar ta ta.
"Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira ta a waya idan basuyi nisa ba sai su dawo".
Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau.
"Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi Mata bayaninsa"
Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da sauri ta mikawa Mai gadin tana fadar "in Sha Allah zan shigo Amma a fada Mata".
"In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida".
Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin tsayawa tana duban kofar da Mai gadin ke kokarin turowa.
"Malam Bismillah".
Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta.
Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa.
"Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare"
"In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode madallah".
Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau.
"Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan su bugun Abuja ba bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai dai in Baki nema ba, ai Nima goben da sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman kamar jira yake.
Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su.
******
Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin kwarewa lokaci lokaci Yana Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin yasa Zahra ta Dan dube shi.
"Wai Ina zamu ne?".
"Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da naje haka nakeyi na duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare na gudu nabar garin daman ba Wanda yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki".
Ya fada Yana wani daure fuska.
Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta ya dauki rawa, duk sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a duniya.
Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara magana bakinta Yana rawa.
Me nayi maka zaka cutar Dani?".
Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta tayi take hawaye suka wanke mata kumatu.
✨✨
✨
AUREN HUCE HAUSHI
Maman Fateemah
Page 26.
________Sai da ya gangare sosai sannan ya kashe motar, chak ya daukota kamar 'yar Baby ya rungumeta, dai dai kunnenta ya kai bakinsa ya hura Mata iska duka tsikar jikinta ta tashi duk da tana cikin halin rudu bai Hana sakon zuwa ba.
"Ki rufa min asiri ada ace satoki nayi Nan da Nan kin rikice nayi Miki Kama da masu irin wannan d'abi'ar? Wlh zolsyarki nakeyi haka Zaki shide min ki Kira min ruwa daga fita unguwa mu bige da kwanan Asibiti cool down idan na sayar ai Nina kashe kaina".
Ba zato taji ya saka harshensa Yana lashe hawayen Yana Wasa da harshensa a saman idanunta, qanqameshi tayi, "Dan Allah ka bari".
"Na bar me?"
"Hakan ba Dadi".
"To da cewa nayi kiji Dadi? Ni nasaka kukan Kinga ai shanye hawayen ya kamani kada muje inda zamu a juya min baya".
Ya fada yana shinshinar gefen wuyanta.
" Kiyi hakuri bazan Kara ba tunda wannan idon naki Mai arahar kuka ne Ni zanga yanda za'ayi idan abin kukan ya samu".
"Cewa fa kayi ka Saba halinka ne ka Saba yin hakan Kuma fa fuskar ka ba Rahama a ciki kamar Mai tsaron gidan wuta".
"Kai innalillahi! Mai tsaron wuta ni din?" ya fada yana fiddo idanu waje
"A'a ba Kai nace ba kamar nace".
"Ba cinya ba kafar baya"
" Nifa nayi ne Dan Naga idonki, idan kina cikin halin tsorata yana sakani nishadi".
Wayar sa ce ta Fara vibration a jikinsa, Dan zameta yayi daga jikinsa ya dauko wayar ya duba tsaki ya d'an Yi.
"Dan matsala kawai".
Ya f