fork ta cako Irish din ta Kai bakinta ta tauna ta hadiye, pepper chicken din ta dauka taci ta dauki kunun Madarar ma ta Sha duk Yana kallon ta shi kuwa Sameer Yi yayi Kamar Allah Bai halicce shi a gurina ba.
Tana gamawa ta tura kujerar da take Kai baya sannan ta dubi shi ido cikin ido tace.
"Gashi naci idan kana tunanin zan zuba maka poison a abinci kayi kuskure lalacewar tawa Bata Kai haka ba, Idan na kasheka wace riba zanci? wato ka tafi lahira free ko? duk lodin zunuban daka dauka niga sakarai na lodawa kaina, to Bari na fad'a maka ba saina aikata zunubi irin haka zan rabu da Kai ba A'a salin alin kowa ze kama gabansa ni da Kai tunda daman masu iya magana na cewa tsintacciyar magen Bata mage nasan komai Daren dadewa zaka koma inda ka fito".
Ta fad'a Tana wurga masa harara ta wuce ta kyalesu batabi ko takan Sameer da yake fadin "Allah ya huci zuciyar amaryarmu".
Da ido Mahmud yabi Zahra har ta bacewa ganinsa "Wai shi yarinya kamar wannan zata saka shi gaba ta fada Masa son ranta amma yayi shiru Yana kallon ta".
Sameer ne ya katse Masa tunanin da yake.
"Dan Allah kada ka koya matsa tsiwa wlh da gani Bata Saba ba, bakaga jikinta har rawa-rawa yake ba".
Ya fad'a Yana kallonsa.
"Jikinta na rawa kenan Kare mata kallo kayi har kaga jikinta na rawa ni ban gani ba?".
"Subhanallahi! Wace irin magana ce haka wlh ba haka nake nufi ba, Bari naje kawai sai munyi waya".
Ya Mike Yana aje rafar dari biyar guda biyu Yana fadin "A bawa madam ace Mata na wuce tunda ka Hana muyi sallama".
Ya biya Kan center table ya dauki keys dinsa yayi gaba tunda yasan ba magana Mahmud ze Masa ba Dan da gaske yazo wuya yanda yanayin fuskarsa ta nuna.
Bayan fitar Sameer, Mahmud kasa ko motsin kirki yayi wai shine tsintacciyar magen? Da gasken gaske maganar ta dokeshi kwafa yayi Yana fadin zakiga tsintacciyar mage iya ganinki sai kin gane bakin rijiya ba gurin wasan makaho babe".
Ji yayi kwata kwata abincin ya fice masa raga Rai duk yanda yake jin yunwa ture abincin yayi ya Mike ya nufi bedroom dinsa Bai jima ba ya fito cikin shigar yari filtex fari dinkin boda da farar hula a Kansa Yana baza qamshinsa na Ibada, yayi waje.
Tunda Zahra ta Fadi maganar dake ranta taji zuciyarta wasai, gefen bed dinta ta zauna tana mita.
"Haka kawai saika wani ringa sakarmin magana ba control duk abinda yazo bakinka saika fad'a mini, Wai na saka wani Abu girkinma ba saina Kara yo da Kai ba sannan na Zama suspect daman saboda A kashedin Ammah ne yasa nayi, kwana biyu amma kamar na shekara duk ka matsa min ka karbe min waya nayi Shiru na Zuba maka ido Naga gudun ruwanka, na fita mikawa bawan Allan Nan abinci kace da izininwa? Haka kawai ka zamar min karfen kafa".
Ta fad'a Tana kwafa.
Tunda gari ya waye Ammah Bata zauna ba shirye-shiryen tafiyar Inna maimuna take wadda zata tafi yau, cikin Shirin fita unguwa Mama ta shigo lokacin Ammar na zubawa innar kilishin da Abba yasa akayi Mata zaunawa tayi tana Fadin "Inna yau zakiyi Mana ta Baki wlh ba dadi".
"Kayya Hajiya Rabi banda abun yazo da sammazi Aida na jima da tafiya gida daga zuwa biki na share our na zauna kinsan da Ardo Yana Raye hakan ba zata faru ba yaushe ze Bari".
"Haka ne Kam Allah yayi musu Rahama".
"Amin" su Inna suka amsa.
Leda mamar ta aje kusa da innar tana Fadin.
"Gashi Inna ba yawa Allah ya kiyaye hanya ni fita zanyi unguwa nasan kafin na dawo kin tafi".
Gdy innar da Ammah sukayi Mata ta tashi tana yiwa innar fatan sauka lafiya.
Sai bayan ta wuce ne innar ke tambayar Ammah ina Hameeda ne Naga tun she jiya da safe bata qara ganinta ba.
"Jiya kina barci tazo Nan Wai ta tafi Jos gurin yayar mamansu larai".
"To ba laifi hakan ba laifi daman shekaranjiya ne da dare na fita zanje can inda na baza ganyen yandi Dana shanya naji uwar tana surfa Mata zagi ban dai San dalili ba Amma naji ita yayar tata tana Fadin sai kije kiba Zahra hakuri Mana tunda kanwar uwarta ce ni dai Nan na barsu Dana dauko shanya ta".
"Allah ya rufa asiri kowa yayi nagari Kansa ya yiwa kuma sharri Dan aike ne duk inda ka tura shi ze dawo, bansan abinda yarinyar Nan ta tsare musu ba, bana raba day biyu da abinda sukasa Hameedar tayi inaga daga baya ta gane Bata kyauta ba shine tayi magana uwar ke zaginta".
Sun Dade suna tattaunawa.
Gurin Sha Sha daya da rabi magaji yazo ya dauki Inna maimunar zuwa gidan Zahra.
Zahra na barci Dan batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba, cikin barcin taji alamar bell din kofa ta yunkura ta tashi ta yafa Veil din rigar saman gashinta.
Tana budewa taga Inna maimuna da magaji, jikin innar ta fada kawai sai ta saki kuka Wanda ita kanta bata San kona menene ba.
" Ke matsa can da Baki rabuwa da shiririta saboda Allah menene abin kuka magidanciya dake, Dan Allah duba min Nan Mai sunan malam wannan ai rashin wayo ne koba haka ba?"
Ta fad'a Tana kallon magaji, duriya yayi Yana fadin "kumfi kusa Inna na bankwana ne tunda Idan Kika shige wannan lungun Sai baba ta gani, ni Naga ma kinyi Rana gaskiya har yanzu Baki tafi ba".
"Ai a Gombe zanyi kwana biyu gidan