Ta fad'a tana share hawaye, Nan da nan hankalin Mamar ya Kara tashi idanunta sukayi jajur, cikin kaushin murya ta Fara fadar.
"Ni za'a yiwa haka wallahi sai dai kowa ya rasa Dan wannan auren sunansa matacce dole ya saketa ko baya kaunar Allah ai indai Ina raye yarinyar Nan sai dai kyanta ya Kare a banza ba dai tayi aure inda zata huta ba ita da hutu sai dai tayi nata gaji da aiki, duk wani haske na rayuwarta saina dusashe shi Bari ma ki gani".
Ta yunkura ta Miki ta nufi bed room dinta tana lalubar wayarta.
Ayi hakuri ba editing Naga kwanaki wata na fadar kada a karanta rubutun ba kyau.
✨
✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨
✨
Story
&
Written
By
Maman Fatimah.
Godiya da yabo sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Amincin su tabbata ga shugaban mu Annabi MUHAMMAD s.a.w.w.
Page twenty two. ( 22)
📖🖋️
________Mahmud Bai bar cikin hotel din ba Saida yayi sallar insha'i, cikin gari ya koma gurin malam lokacin sun Fara karatun dare da maza manya Kamar Yanda suka Saba, shima littafin ya dauko na Riyadussalihinp ya zauna daukar karatun sai gurin takwas, bayan jama'ar sun watse ya rage daga malam din sai Mahmud da Habib.
Ganin Mahmud din ya zauna malam yasan da magana, Saida Habib ya gama gyara littatafan kusan aikinsa ne shida Abubakar, bayan fitar Habib din kusa da malam din Mahmud ya matso Yana Fadin Baba barka da dare".
Cikin sakin fuska malam ya amsa Masa Yana Fadin.
"Ya akayi ka zauna har wannan lokacin baka koma ba kasan ba sabawa tayu ba itama ya kamata a ringa kula". Kai yadan Sosa Yana Fadin in Sha Allah yanzu zan tafi daman na tsaya ne Ina son muyi magana".
"To Babu laifi ina saurarenka".
Qara sadda Kansa yayi Yana Fadin.
"Daman game da maganar tafiyar da zamuyi ne nace ko za'a samu wadda zata zauna da yarinyar Nan ne?".
Gyaran murya malam din yayi kafin yace
"Eh hakan yayi dai dai saidai ka tuntubeta kaji nata ra'ayin tunda Naga gidan nasu da wadatar juma'a ko wata zata tayata zaman tunda kasan sha'anin yau sai a hankali kada a Kai Mata wadda za'a samu matsala".
Tunda baba malam ya fara Kora bayani Mahmud ke gyada Kai sai da ya Kai Aya sannan Mahmud din yace. "haka ne in Sha Allah zan nemi shawarar tata duk yanda mukayi zan fad'a maka, na gode" Ya fada kafin su fad'a wata hirar akan wani sabon project da suka samu daga usaid karshi gwamnatin jihar Bauchi da sukazo musu aikin plane na shekara bakwai. Bashi ya bar gurin malam ba sai wurin Tara da rabi, daya fito ma majalissar su ya nufa gurin su salisu Nan suka dunga yi masa chari akan ya zagaye ya tafi gidansa bai nemi rakiyar kowa ba ko rowar ganin Amarya yake musu, shi kuma ya Kare kansa da hujjar Shima be San da zuwenta ba kawai da yamma Baba malam yace yaje can gidan ya jira Alhaji Jafar Yana son ganinsa, Yana zuwa kuma ya ganshi da zahrar ya kawota da kansa, to wa zaya Kira Kuma ihu bayan hari.
Sunyi masa Allah Sanya Alkhairi da Alkawarin zuwa su gaida amarya sai goma ya karbi lifan din Habib ya nufi hayin banki.
Lokacin daya shiga falon shiru ba motsin komai sai ni'imtaccen kamshin turarukan wuta 'yan asali da kuma na roomfreshner masu dadin kamshi lumshe ido yayi Yana shakar kamshin.Nan da Nan yaji wata irin kasala ta rufe shi ga wani mahaukacin feeling yana bijiro masa tun bayan barinsa gidan yake fama da wani irin tunanin ta duk motsin da zeyi sai ta fado Masa,moment din yake tunawa duk da ba cikin dadin Rai yayi ba Amma ya tsaya Masa a zuciya sosai Kamar magnet haka ya d'afe Masa.
A hankali ya taka zuwa tsakiyar falon komai tsab Kamar wani mahaluki Bai shiga falon ba, harya Fara Hawa steps din da zasu sada shi da bedrooms nasu hankalin sa ya Kai wurin dining din manyan warmers ya gani a hankali ya sauko ya nufi gurin abinci ne mai rai da lafiya sai Kuma pepper soup na cow tail da hadin salad da alama na ba'a taba ba yasan aikin Ammarta ne kada kai yayi Yana fadin "wato abincin ne bazataci ba ko me take nufi? baiwar Allah ta Bata lokacinta ta bada a kawo Amma ba za'aci ba"
Dakinta ya nufa Yana zuwa ya kama handle din yaji ta a rufe, shiru yayi wata zuciyar na cewa yayi knocking wata Kuma na kwabarsa, juyawa yayi ya koma gurin dining din shi dai baze iya cin abinci Mai nauyi ba, abincin ya dauka yabar pepper soup da hadin salad din tinda bashi da yawa.
Gurin Mai gadi ya nufa yana Fadin "Ga abincin nan a samu ayi amfani dashi yayi yawa".
Da hanzari ya taso Yana fadin "To yallabai ai dazu ma Mai gidan ta Aiko dashi har Saida na bawa wasu Yara ma sauran, wannan kuma Bari na kira Mustapha yazo ya kai musu can gida madallah dai an gode da dawainya".
"Haba ba komai gashi idan yazo sai ya biya mashin dasu". Ya aje Masa 5k akan warmer din ya juya yabar Mai gadin Yana sheka Masa addu'a da fatan Alkhairi.
Saida yayi wanka sannan ya dawo dining din yaci iya Yanda yake ganin ya isheshi sauran ya Kara kaiwa Mai gadin sannan ya koma daki.
Kan kujerar desktop computer ya zauna Yana kunnawa da ita akayi masa connecting din CCTV din da