nta daya ya koma inda ya sauke Mata kudaden masu yawa ya Kuma yi Alkawarin gabatar da kansa gurin iyayenta tunda bada Wasa yazo ba, itama Kuma Bata Hana ba tunda da gaske taji yes zata iya rayuwa dashi idan Allah ya amince.
Bayan barowarsa kasar da sati daya ya gabatar da kansa ga Alhaji Jafar a matsayin Mai son auren Zahra, Bai rufe Masa komai ba har zuwan da yayi syprus din,sai dai ya bashi hakuri akan zuwan daya Farayi kafin yazo gare shi, ba komai Alhajin ya nuna masa sai dai yace irin hakan bashi da kyau kodon gaba mutum yabi 'ya mace wata uwa duniyar batar da sanin magabatanta ba akwai hadarin lalacewar tarbiyya ga Wanda Allah yasa shaidan yafi karfin zuciyar su.
Alhajin yayi Masa tambayoyi sosai akan Sana'a da Kuma asalinsa, sannan ya fada Masa shima mahaifinsa ya rasu tun Yana level one hundred a jami'a, a labarinsa daya fada masa nan ya gano kanin mahaifansa sunyi makaranta tare dashi a Bauchi.
Bayan tafiyar Musbahun da Alhaji Jafar ya tada mutum takanas yaje har Kano da taimakon abokinsa Alhaji Muttaqa akayi Masa bincike kan Mushahu Kuma Alhamdulillahi ba'a Sami wani abun ashsha ba a tare dashi Dan mahaifiyar ma ta fito ne daga cikin manyan gidajen sarautar Kano.
Bangaren Zahrar kuwa kusan Kullum suna tare da Musbahun a waya Dan har ya haddace lokacin agogon kasar, tun tana daridari har ta sallama tare da karfafawar su Sajida kafin su gama semester din sun shaku dashi sosai Bata rufe Masa matsalar data fuskanta a baya ba, nuna Mata ma yayi rabonsa ne ya kawo aka ringa samun akasin na bayan ya Kuma yi Mata Alkawarin ruwa da iska ba abunda ze girgaiza tarensu bare har akai ga rabuwa Koda kuwa Aljani ne ya aurata in sha Allah sai yaga bayansa, yayi Mata alkawura da dama ya nuna Mata Babu wani abu da ze girgaiza shi koya bashi tsoro akan lamarin aurenta.
Magana tayi nisa Dan har iyaye sun shiga abinda yayiwa Ammah Dadi kenan Dan wannan karon Kam Zahra tayi Dace da Dan manyan mutane sosai, dan basu bar garin ba Saida suka shaida lokacin aure idan ta gama service da wata daya duk da sunso ayi bikin kafin tayi service din sai Alhajin ya nuna musu suyi hakuri tayi idan ta gama saita zauna guri daya ba daga kaita ba ba dadewa ta Fara fita kullum, Kuma ya Hana kayan lefe Dan Alkawari yayi ankawo biyu an karbe to kuwa ko waye zata aura sai dai ya aje Mata kayan idan taje gidan ya Bata.
Lokacin dasu Zahra suka Gama karatunsu har da Ammah da Hameeda akaje bikin graduation dinsu mutanen Jordan ma sunje har Mama Hanifa.
Bayan kammala taron sun Kara kwanaki a kasar, Zahra ta raka Hameeda kuraren shakatawa da yawa tayi kallo tayi santin inama Abba ya dawo dasu Nan Suma gashi ita har ta Gama Amma su Kullum karatunsu ba cigaba ana faman strike tunda a yanzu ma shine ya dawo dasu gida har ta samu damar zuwa itama.
Ranar da zasu taho sun Sha kukan rabuwa dasu Sajida tunda su saura shekara daya su gama.
Murna gurin Zahra ba magana ji take kamar ta sauke wani abu Mai nauyi daga kanta.
Musbahu yaso zuwa graduation dinsu Zahrar Amma lokacin Yana busy yaje wani special assignment a Kenya dole sai hakuri yayi, Amma Yana dawowa ya yiwa Azare dirar mikiya a ranar Zahra taga zallar so a gurinsa Dan ji yake kamar ya dauke ta yayi gaba da ita, itama ta bashi kulawa kamar me,Hameeda tazo sun gaisa sun Dade suna Hira dashi tambakar sun shekara da sanin juna, sunan mujiba ma ta shigo suka gaisa ba shi yabar Azare ba sai kusan magariba Dan ma Zahrar nata Masa magiyar ya tafi saboda rashin tsaro irin na kasar.
Tun daga lokacin hanya ta aure shi tsakanin kano da Azare. Mushahu na mutane ne kusan duk Wanda ya kwana ya tashi a Nan kukkuken unguwarsu Zahra yasa shi Koda kuwa ba gaisawa suke ba, wata kila ya taba yiwa wani alheri a cikin yaran gidanku Dan da gaske hannunsa a sake yake gurin Alkhairi.
Sunyi sabo sosai da jama'a a Nan har gurin malam Bukar Yana zuwa sauda dama idan ya shigo garin, wasu ma daga cikin samarin gidan malam din sunyi sabo sosai.
Lokacin da results dinsu Zahra ya fita Sam bataje ba Auncle Haisam ne yayi Mata komai Allah ya taimakeka ta fito da first class degree a akan anatomy.
Allah ya taikata da taimakon Ya Hassan aka kawota bauchi service, bayan zaman camp sukayi posting dinta Dr Sulaiman Adamu memorial college of Hygiene and Environmental health science Azare.
Ammah taji dadin hakan sosai haka shima Mushahun yaso hakan kwarai da gaske.
Zahrar najin dadin aikin sosai da sosai domin teaching Yana cikin hobbies dinta.
Bayan sun Gama ne da wata daya kamar yanda akayi Alkawari aka Fara kokarin Fara shidimar bikin ta dai dai lokacin Kuma akayiwa su Ummee rasuwa a saudiyya abinda ya Hana su zuwa kenan da har Ammah tace a daga bikin tunda rasuwar ta jikinsu ce kanin Baban Ummeen ne ya rasu,Amman sai sukace Dan me ayi idan komai ya lafa zasuzo suga daki kawaii.
A satin da za'a Fara bikin kusan Kullum Mushahu da Abokansa shakikai su Deeni da Aliyu Wanda Suke cussings suke ta zirga-zirgar ganin abubuwa sunyi yanda ake so duk wasu programs a nan za'ayi dinner ce kawai zasuyi a Kano, sun Kama d