anzu ma harkar kasuwancin ta kawo shi kasar. Zahra ma ta fada Masa sunanta da inda take karatu da Dan zaman da zatayi anan kasar kafin ta wuce.
Bai bar airport din ba har Saida Mama Hanifa tazo daukar zahra, da yake Mushahun wise ne sosai ya sake da Mama Hwnifar don Basu rabu ba har Saida ya karbi address din gidanta, saida suka bacewa ganinsa sannan Shima ya nemi taxin cikin airport ya nufi hotel din da yake sauka idan yazo kasar da buri kala kala a zuciyarsa kan Zahra.
Satinta daya ata nufi syprus kafin lokacin Mushahu ya Kai Mata ziyara yafi sau hudu ba karamin samun shiga yayi a gurin Mama Hanifa ba.
Zauwanta makaranta da kwana daya Sajida da Khadijah da Fatima suka dawo Anisa ce Bata dawo ba suna Umara da Yayarta sai Kuma sukayi Dan Samu matsalar visa.
Karatu Suke ba Kama hannun yaro Koda yaushe suna busy da karatu, tunda Zahra ta rabu da Musbahu a turkey Sam ta aje batunsa a gefe duk da kusan Kullum saiya kirata sun gaisa Yana ta kafa gwamnatin sa a gurinta. Bazato ba tsammani ranar wata Saturday taje weekend gidan Uncle Haisam ya kirata da number din kasar Yana fada ya shigo kasar tayi jiransa Nan da awa daya ze shigo makarantar, ba karamin mamaki tayi ba da jin hakan, dan harga Allah batayi zaton da gaske yake ba da yace Mata Yana Nan zuwa syprus din.
Nan da Nan ta fadawa Aunty Jinan matar uncle zata koma school yau suna da wani group Assignment data manta zasuyi ta taho, Bata Hana ta ba tunda Daman uncle din baya kasar sunje wani aiki south Korea, snacks Aunty jinan ta hada Mata masu yawa ta tafi dasu. Allah ya taimaketa ta fito da card dinta na shiga bus ko train, mintina talatin masu kyau suka kawota kyrenia city.
Lokacin data shiga hostei dakinsu ta wuce ta Kara gyara jikinta.
Wani karamin basket da dauko ta zuba snacks da drinks masu sanyi, turare ta Kara fesawa har Brandy wadda Suke daki daya take tambayar ta ko zataje wani park ne ta huta yau weekend?
Eh kawai tace Mata tayi gaba ta fita daga dakin, gurin su Sajida ta nufa akayi rashin sa'a duk basa Nan sai Anisa kawai ta Samu tana sallah.
Zama tayi tana tunanin yanda lamura Suke ta juya Mata kamar a almara ko wannan din shi ya zata Kaya a kansa? Dan haka Nan taji bazata iya yi Masa rashin kirki ba Dan duk Wanda ze Bata kudinsa da lokacin sa ya biyoka har wata kasar duk da baka bashi fuska ba to kuwa Bai cancanci wulakantawa ba a gurinka.
Kafin Anisa ta idar da sallar wayar Zahrar tayi Kara alamun Kira ya shigo, number dazu ce ta daga tayi sallama, daga can ya fada Mata ya shigo ciki da inda yake.
Bayan sun gama wayar ne Anisa ta idar da sallar ta kalli Zahrar tana fadin "yaushe Kika dawo nayi zato sai Monday da safe Zaki dawo?".
"Ke dai Bari kawai wallahi guy din Nan Dana fada muku mun hadu a airport din Kano Yana kallona har ya bini gidan Mama Hanifa?"
Kai Anisa ta gyada alamar ta gane.
"To shine fa dazu ya kirani Wai gashi a kasar ya cika Alkawari zuwa anjima ze shigo Nan gurina, shine yasa na dawo yanzuma kiransa ne ya shigo Yana gurin garden din can na gurin second gate".
A gurin suka same shi Yana tsaye kusa da wani kangaroo na siminti Yana kallonsa har da kanana a kusa dashi yayi kyau sosai kamar na gaske, ya shagala da kollon har baisan sunzo gurinsa ba Saida Anisa tayi Masa sallama sannan hankalinsa ya kawo kansu. Wani irin mahaukacin kyau yaga Zahrar ta karayi a idonsa, kasa dauke idanunsa yayi daga kanta. "Masha Allah!"
Ya furta a hankali Yana fadada fara'a akan fuskarsa tare da amsa sallamarsu.
Karkashin wata bishiya Anisa ta nuna masa inda akayi kujerun sumunti masu kyau sosai, bayan sun zauna ne Anisa ta gaishe shi tana Masa ya hanya, sannan Zahra ta gaishe shi itama, duk sai taji duk wani iri saboda Sam lamarin maza gaba daya ya Gama fuce Mata daga Rai duk da bazata ce sun yaucareta ba Amman lamarin su a gurinta Mai girma ne Dan duk yanda taso ta manta abunda ya faru a baya Bata iyawa, Samun kanta tayi da wani irin Jin bazata iya watsa masa kasa a ido ba.
Sun jima suna tattaunawa da Anisa a fakaice Yana yiwa kansa campaign a gurinta, Anisar ta gabatar Masa da abubuwan da suka kawo masa, ita dai Zahra tana jinsu suna ta Hira kanta na kasa tana Dan Wasa da wani zoben white gold da Aunty Nawwara ta saya Mata lokacin da sukaje Umara.
Anisa ta jima sosai kafin tace zataje ta duba idansu Sajida sun dawo.
Bayan tafiyarta Musbahu ya yayi duk yanda zeyi ya janyo hankalin Zahrar ta sake dashi Kuma Alhamdulillahi kafin wani lokacin ta Dan sake ba kamar lokacin da suka zoba, a nan yake fada Mata shifa da gaske yakeyi yafi son kafin ta Gama makaranta a Gama komai tana gamawa kawai ayi bikin tayi service a gidansa. Saida aka dauki lokaci sosai sannan su Sajida suka karaso gurin bisa jagorancin Anisa, sun jima suna Hira sosai anan yake fada Mata Shima Dan kano ne sokoto road, ita Kuma ta fada Masa tana Jambulu Amma da suna zaune a Gwammaja ne.
Ya jima sosai kafin ya tafi,washe gari Sunday yaso su fita Amma Zahra ta nuna ba wannan maganar duk yanda yakai da naci ta Kiya har su Sajida suka saka Baki Amma ta qiya. Sati