ana cewa gata Nan Amman sai tayi burus da zancen.
Har dai ta Kai Ammah karshe tayi magana. Hameeda tace ta rakata suje tare, yau gurin malam din ba kowa ba Kuma rumfar karatu tunda ranar basa karatu. Gurin ganawa da mutane suka sameshi su Habib suna ta gyaran Shirin kantar littafai.
Da sallama suka shiga suka gaishe da malam din sannan suka gaishe dasu Habib, sai sukayi shiru.
Malam ne yace "Zahra'u Ashe lokacin komawar taki har yayi ko?"
Kara risinawa tayi tana fadin "eh lokacin yayi yayi Baba gobe zan tafi in Sha Allahu amma a Istanbul zan tsaya sai wani satin zan wuce syprus din".
"Masha Allah. Allah ya taimaka, ki Kara hakuri akan lamuranki duk wani bawan Allah na kwarai sai Allah ya jarabce shi Dan ya gwada imaninsa ki dauki abinda yake faruwa dake Daman haka Allah ya rubuta Miki taki kaddarar kada ki yanke kauna daga Rahamar Ubangiji. Ga addu'oi nan da littatafan addu'a ki tafi dasu ki ringa yinsu Kuma kada a shagala da ambaton Allah a duk inda aka Sami kai, Allah yayi Albarka ya bada nasara ya kiyaye hanya".
"Allahumma Amin suka fada a tare".
Habib malam ya yiwa magana ya Miko ledar da aka saka sakon nata, Hameeda ta karba suka Kara yiwa malam godiya suka fito suka shiga cikin gidansa Zahra ta Kara duba jikin iya Abun ta Kuma yi Mata sallama.
Basu koma gida ba, gidan su mujiba suka shiga Bata Nan ma sai Maman ta suka barwa sallahun tafiyar zahrar suka nufo gida, sunzo dai dai masallacin gidansu ne sukaga Ya Abdul Hakeem da Dodon Zahrar a zauna a kan carpet karami a gefen masallacin suna hira Kai da gani da kyakykyawar alaqa a tsakanin su.
Gaishesu sukayi suka wuce, Hameeda ce ta kalli Zahra tana fadin "Kinga wancen Guy din yanda Salma ta mutu kansa ba magana! lokacin data Fara ganinsa munzo hutu wallahi kamar zata zauce akansa sai da Mama ta taka Mata burki taci Mata mutunci akan ta rasa Wanda zata so sai Almajira Wanda ba'a San asalinsa ba, duk yanda taso ta nunawa mamar wannan da banbancin da irin Wanda ta sani amma Sam taki fahimta Dan har so tayi tayi Mata duka tana fadin Dan lalacewa ta rasa Wanda zataso sai fakiri Mai allaziwahidin Dan salon Abba yaji ya Goya Mata baya tunda Wai ance sune suka kawo shi garin bandai San kan labarin ba gaskiya". Ita dai Zahra Bata tofa tataba daga uhm sai umh umu uhm, har suka karasa gida.
A Daren sun raba dare suna Hira da Ammah a Nan ta dunga yi Mata magiyar ta daure taje gurinta ko zuwa karshen shekara ne ta ganota ba ta tura Mata Ya Abdul Hakeem ba.
Karfe shida Mai kyau sun dauki hanyar Kano ita da Ya Abdul Hakeem da Hameeda da magaji.
Nan suka zauna da zahra suna ta Hira kafin lokacin tashin su yayi, in da wani Abu da ya damu Zahra a gurin Bai wuce kallon da wani matashi ya kureta da Shi ba, duk inda zata dago Kai sai sun hada Ido dashi, Sam ya hanata sakat da idanunsa idan ba idanunta kemata gizo ba har wani lumshe ido yake da wani kankance su. A haka har lokaci ya cika aka Fara shiga jirgin hand bag ce kawai a hannun Zahra tunda kayan an tafi dasu tun zuwansu lokacin da ta juya ta Fara tafiya ba zato taji hawaye a idanunta abinda ta dunga kokarin kar tayi kenan tun daga gida lokacin da Auta Musaddiq ya fasa Kuka da suka taso Amma sai gashi ta kasa jurewa itama Saida suka zubu, juyawa tayi kadan lokacin da zata hau steps din sai taga Ya Abdul Hakeem ya Kama hannun Hameeda sun juya sun Fara tafiya tana share hawaye da dayan hannun itama ta juyo hannu Zahra ta dago Mata alamar bye sannan ta Haye zuwa ciki.
Kusa da wata Mata ta zauna da alamar kamar zatayi sa'ar Ammah, ta gaisheta.
Saida jirgin ze tashi ne taji na gefenta Yana fadin "duk tunanin gidan ne ya hanaki jin sanarwar a daura belt da ake ne?" Ya fada in a soft voice. Dago Kai tayi ta dubi Mai maganar dake gefenta, wannan Wanda ya dameta da kallo ne kafin su shigo, ita Sam batama San sanda ya zauna kusa da ita ba.
"Nagode" ta fadawa tana saka belt din lokacin da jirgin yayi balance a sama ne ta cire belt din ta bude computer dake jikin kujerar dake gabanta tana kallon location din da Suke bi tun tana Gane garuruwan data sani ko take jin sunansu har aka shigo Wanda sai dai ta karanta kawai. Jefi jefi suna Dan magana da matar dake kusa da ita. Nan kusa da ita dai Bata Kara kallonsa ba tunda taga shi kallon mutane kamar dabi'arsa ne.
Sanyi kamar tafiyar awa daya taji yana Mata magana da farko yi tayi kamar bataji ba, Saida matar dake kusa da ita tace "bakyaji ba ana Miki magana, ko kina da aurene?".
Kai ta girgaiza alamar A'a.
"To meyasa kina Jin Yana Miki magana Kika kyale shi? ba Dadi irin haka baka wulakanta mutum ba kasan gaba abinda Allah zeyi ba kinji".
A hankali take Mata maganar yanda ita kadai zata iya ji.
"Tom nagode in Sha Allah zan kiyaye". ta fada mata.
Bai hakura ba har Saida ya Sami kan Zahra duk da ba wani sakewa tayi dashi ba Amma dai hakan yayi masa.
Lokacin da suka sauka haka ya dunga bin Zahra kafa ya kafa har ta dauko kayan ta da aka gana screening suka fito, a Nan ya fada Mata sunansa Mushahu shi Dan Kano ne Yana aikin government Yana Kuma kasuwwnci y