t student na kowane department award.
A karshe semester din ne aka hada taron Wanda ya Tara al'umma daban daban daga kasashen duniya masu Taya 'ya'yan su da 'yan uwa murnar gama karatu, celebration ne ake na gasken gaske, su zahra dai suna kallon abubuwan tunda wannan shine na farko da akayi suna Nan lokacin da akazo bada award ne ba zato ba tsammani aka Kira zahra Muhammad sani daga Nigeria aka Bata award na overall a department dinsu akan kowane subject.
Wayyo murna gurinsu ba'a magana Dan Zahra kuwa har mukan Dadi tayi data duba taga yawan daliban da suke a department din nasu Amma ace ita ta karbi best ai abin murna ne Kam. Sun Sha hotuna da mutanen mu na africa more especially 'yan Nigeria.
A ranar Zahra tayi takaicin karatun nesa da ace a gida ne da Abbanta ko Ammah ko wani daga cikin yayinta zata danqawa kyautar su sharing happiness din tare Amma Nan kuwa fa sai da friends da wasu tsirarun mutane Wanda ma ba saninsu tayi ba sukayi farin cikin, ga Uncle Haisam ma a matarsa da yaran duka sun tafi turkey.
Sai ta waya sukayi murnarsu da jama'ar gida ta tura musu hoton award din ta waya hotunan da suka dauka.
-----------------
AZAREN KATAGUM
Alhaji Jafar ne da Malam Bukar sai Habibu dan kanwar malam Bukar dake aure a suleja malam din yake rikonsa tun yana karami mahaifinsa ya rabu da mahaifiyar sa acan gida Yobe da tayi auren a suleja din ne baban Habibun yace baza'a tafi Masa da yaro gidan wani ba yayi agolanci, rigima sosai aka kwasa da shi saboda itama tace bazata bar danta a inda za'a kashe Mata shi ba. Shine mafarin malam din ya dauko shi tunda ba wasu 'ya'ya yake dasu da yawa ba, a hannun malam ya girma shi yayi karatun boko har matakin HND.
Jikamshi malumfashj zasuje Daurin Auren 'yar abokin Alhaji Jafar din sannan zasu shiga Jikamshi dubiyar malamin malam Bukar din daya kwanta kwanakin baya a Asibitin Ibadan nisa yasa shi majiyyacin ya Hana masu zuwa dubiya sai yanzu daya dawo gida ne malam zeyi amfani da wannan damar yaje dubiyar.
Tafiya ce mikakkiya Dan tsakanin Azare da malumfashi tafiya ce ba kadan ba Dan haka sukayi sakko Habibun ne ze tukasu malam Bala anyi Masa Rashi acen garinsu Itas gadau Yana can.
Cikin ikon Allah Basu rasa Daurin auren ba Dan Sha buying Mai kyau suna cikin garin malumfashin.
Basu Bata lokaci ba suka dauko hanya sun biya jikamshin sun duba malamin Alhaji yayi masa kyau ta girma.
Suka dauki hanya sosai Alhaji Jafar ya yaba da tukin Habib Dan baiyi zaton ya kware irin haka ba.
Sunzo kachako lokacin sallar la'asar yayi guri suka Sami inda akayi wani Dan masallaci dan matafiya.
Suka firfito Dan gabatar da sallar, malam ne ya Fara gewayawa yayi dahara sannan Shima Alhajin yayo sukayi alwala suka shiga sallah Saida suka Gama suka fito sannan Habib Shima ya nufi gurin you daharar Amma shi saiya nufi wani bangaren daban, Bai jima da tafiya ba sai gashi da sauri Yana Kiran" Baba malam! Kuzo ku gani". Da sauri suka nufi inda yake harma da wani mutum da suka Sami a gurin Kamar Mai kula da gurin ne Dan daga gefe da 'yar tiredar shi suka rankaya Habib na gaba suna bin shi tun kafin su karasa suka hango mutum a kwance Kamar marar Rai.
"Subhanallahi "abinda suka gada kenan suna karasawa kusa dashi sai da suka matsa sosai suka Gane da ransa Amma Yana cikin wani yanayi, dako dako sukayi aka rasa ya za'ayi dashi matashi ne ba zefi sana'an Habibun ba saidai a yanayin yanda jikinsa yake ba alamar wahala a tare dashi. Habib ne ya matsa kusa dashi sosai ya tsuguna Yana dudduba jikinsa ko akwai alamun duka ko makamancinsa amma babu komai, shawara sukayi su daukeshi kodan ceton Rai su tafi dashi idan yaso sai su dauki hotonsa a Dora a social media wata kila a Dace.
Lokacin da suka shigo Azare ana sallar insha'i directly asibiti suka nufa dashi ma'aikatan nan da Nan suka duqufa a kansa, sai gurin Sha daya Allah ya taimaka ya kawa kwakwkwaran numfashi.
Sai lokacin suka nufi gida malam ya turo dalibansa guda biyu ya fada musu dakin da aka kwantar da Wanda suka tsinta din, ya basu kudi saboda abun bukata.
Haka su Abubakar suka kwana da shi sai gurin hudu da rabi na Asuba ya bude idanunsa Yana kallon bakon gurin da yake ciki ga bakin mutane a gurinsa, yukurawa yayi ze tashi yqji ya kasa kansa Kamar an Dora Masa dutse, bakinsa ya bude zeyi magana yaji kwata kwata ya kasa yayi yayi Amma Sam maganar taki yuwuwa sai hakuri yayi ya zuwa bawa sarautar Allah ido.
,💋❤️
💋❤️
AUREN HUCE HAUSHIN
💋❤️
💋❤️
✨ MAMAN FATIMAH ✨
✨PAGE THIRTEEN ✨(13)
__________Washe gari daga gidan Alhaji Jafar Abdul Hakeem da magaji suka kawowa su Abubakar abinci Asibiti, sun tausaya bawan Allah nan sosai Dan zuwa lokacin sun fuskanci baya magana Kuma jikin ma baya motsuwa yanda ya kamata, toilet ma sai da sukayi Kama Kama suka kaishi, a haka su malam suka shigo Asibitin tare dasu Malam Mudi, Basu Dade da zuwa ba likitoci suka shigo round sun tambayi menene Asalin ciwon to su dai sun fada musu Yan suka h