NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 134 of 136

a barci nakeji tunda kin hanani barci da fitinarki". Rigar ya zuge zif din ya cire mata ita ya barta daga ita sai undies kawai ya dauketa can ya nufi bed din da ita tana mutsulmutsultun ya sauketa ya kiya Saida ya dangana ta da saman bed din, shima jallabiyar ya zare ya janyota ya lullubesu da gaske barcin za'ayi Dan tunda ya sakata a jikinsa Bai Kara yi Mata komai ba. *** *** *** Tunda Ammi tayi sallah Bata Koma barci lazimi ta zauna tana yi amma zuciyar ta Babu dadi kwanan nan kusan Kullum sai tayi mafarkin Mahmud da wata yarinya budurwa Yana rike da ita da hannu Daya dayan Kuma Yana ta faman fada da wasu irin halittu mara kyawun gani, to yau ma shita Karayi Saida taga wasu mutane dattijai guda biyu sunzo sun Taya Shi kashe wadannan halittun sun tasa su shida yarinyar har wani gida sai da suka shige sannan suka juyo suka tafi. A haka Mai gidan ya sameta Saida ya zauna ya Kare Mata kallo yasan da akwai damuwa a tare da ita sai dai tana kokarin biyewa. "Ammin Yara me yake damunki duk kwanakin Nan Baki da walwala Sam ko kula dani ma tayi baya ko Baki huce bane har yanzu?". Kai ta girgiza "A'a kawai dai lamari Hussain ne yake damuna kofa da Rana Daya Bai taba kirana ba ko sako ta email Bai taba Yi min ba, gashi a kwanakin nan sai wasu irin mafarkai nakeyi dashi marasa dadi abinda yafi tsaya min a Rai Kullum da wata yarinya budurwa kamar 'yar India nake ganinsa da ita Ina tsoron wani Abu wallahi na rasa yanda zanyi Dan Allah kayi wani Abu akai". Sai hawaye sharrrr. "Subahaballahi! Haba zainab ya Zaki ringa yi Masa kuka kinsan masifar zubarwa da d'a hawaye kuwa ko wani abun yake aikatawa ai saiya karu idan kina Masa kuka, addu'a zamuci gaba da Yi Masa nifa jikina Yana bani Yana Dubai Dan last week na samu leakage akan Yana can din Dan yayi wasu ziyarorin bazata a can harya dakatar da wasu ma'aikatansa sai dai duk kokarin a gano min masaukinsa sabo hakan yaci tura Dan ba'a inda yake sauka ya sauka ba tunda gudun hijira yayi". Hawayen ta goge ta tashi tana ninke sallayar ta zauna kusa dashi. "Shikenan Allah ya shiga cikin lamarin ya kureshi daga sharrin zinace zinacen zamani wallahi badan komai nufin Allah bane Wanda yaso yake bawa kyautarsa danace dama bashi ya samu wannan budin ba da kananun shekaru to yanda yaso haka yake tsara kayansa, Amma ga yayunsa Nan ba Wanda ya takura musu Suma ai suna da wadatar,tunda Allah yayi muku karfin arziki waye talaka a cikin family din nan?". Dan murmushi general yayi Yana kallon yanda take fadin magana abinda ba halinta ba inda akan twins ne sai dai wani yayi magana Amma ta zage tana fadin son ranta. "To ya zamuyi da hukuncin Allah shi yaso ya daukaka a cikin zuri'ar da Wanda ya Isa yace a'a Ina cewa Alhaji Ishaq ne ya bashi jarin Daya Fara sana'a dasu tun Yana hannun Hajja, Amma yanzu zaki hada arzikinsu ko kusa ko alama Babu Hadi,.koni Dana haifeshi ya mallaki abinda bani da kwatqnkwacinsa, Keda Kika haifeshi kin mallaki abinda yake dashi? To kiyi istigifari ga Allah tunda shine yace Yana azurta Wanda yaso ba tare da hisabi ba,ai kin gane?". "Na gane Allah ya Zama gatansa a duk inda yake,Amma fa yarinyar Nan ta tsaya min a rai idan Yana kusa da wannan ai zai manta da kowa ne tunda cikin bacin rai yabar gida ga Kuma kudi a tare dashi kaga sai Allah kadai ze kare shi". Dariya ta bashi sai da yayi sosai kafin yace. *In Sha Allah in dai Zina gado ce to Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w zuri'ar mu bazasuyi ba Ni ba mazunaci bane haka kema ba ita bace in Sha Allah.Allah baze jarabcemu da ita ba, Kika sani ko bushara ake Miki ke uwa kin samu sirika". "Haba dai har abun ya Kai haka yayi aure ba sanin iyayensa ai kuwa da lamarin ya lalace". 'yar dariya yayi. "Kedai kije ki shirya min breakfast daurin Aure zamuje kabba na Dan gidan sanata Abdul Aziz" "Ok.bari na shiga kitchen din" Ta tashi ta fice tana baza kamshinta as usual. ****** Tun idar da sallar Rukayya ta taso ta nufo part din da zahra ta kwana,abin mamaki an canza pin kofar dan ta kwada yafi sau goma Amma taki budewa. Nan da Nan taji hankalin ta ya tashi me Kenan badai wani bane ya shigewa 'yar mutane ba gashi jiya Taki Kai Mata wayarta da ba saita kirata ba, gudun kada tace sai sun kwana ya hata ta Kai mata. Number ya Sameer ta lalubo lokacin Yana barci, Yana dauka ko gaishe shi bata tsaya yi ba ta Fara fadin "Ya Sameer ka taimakeni wallahi tun sassafe bake kokarin shiga part din da zahra take Amma kofar kofar kamar an canza pin din na saka yafi sau goma Amma yaki budewa". Tsaki yayi "Waike Dan Allah Ruky yaushe Zaki girma ne? to oga ne ya shigo cikin dare Nima da asuba naga text message dinsa Dan haka ki Zama ready idan na shigo saimu wuce tare Amma yanzu kada kuyi komai za'a kawo abinci". "To ai su Iya Rahane har sun kusa gamawa baka fada min ba tun dazu". Ok, ba komai sai a hada tunda gidan da jama'a, yauwa zuwa an Jima ki bude musu part din Nan na kusa da parking lot sai su zauna a nan tunda shima ogan Bai san ze shigo kanon ba harsu Gama su koma to matsalar madam din c
🏠